• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BAYAN ZAƁEN FIDDA-GWANI: Ko ministocin Buhari da su ka faɗi zaɓe na da sauran tudun dafawa?

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
June 14, 2022
in Babban Labari
0
Talauci, rashin aikin yi da rashin tsaro suka sa zan yi takarar shugaban kasa domin in kauda su a Najeriya – Amaechi

Makonni biyu bayan kammala zaɓen fidda-gwanin takarar shugaban ƙasa na APC, tuni har an fara tambaya da tuninin makomar ministocin Shugaba Muhammadu Buhari, waɗanda su ka ajiye muƙaman su, su ka shiga takarar shugaban ƙasa.

Daga cikin Ministocin Buhari, waɗanda su ka shiga takarar sun haɗa da Karamin Ministan Ilmi, Emeka Nwajiuba, Ministan Harkokin Kimiyya da Fasaha, Ogbonnaya Onu, sai Ministan Harkokin Sufuri, Rotimi Amaechi da kuma Ministan Harkokin Bunƙasa Yankin Neja Delta wato Godswill Akpabio.

Sun lale Naira miliyan 100 kowanen su ya sayi fam na takara. Yayin da wasu sun janye ana kusa da fara zaɓe, Amaechi bai janye ba, ya samu ƙuri’u 316, kuma shi ya zo na biyu.

Akpabio ya janye daidai lokacin da ake shirin fara zaɓe. Sai dai kuma wakilan zaɓen ‘yan takara na jihar Akwa Ibom su 91 ba su samu iznin jefa ƙuri’a ba, saboda dokar kotu ta haramta masu.

Daga cikin ƙuri’u 2322 da aka jefa, Ogbonnaya Onu ya samu ɗaya tal, sai Emeka Nwajiuba shi ma ɗaya tal ya samu. Dama kuma ko filin gangamin zaɓen bai je fa.

Yayin da ministocin huɗu su ka rasa muƙami kuma su ka rasa takara, su zuma zaɓaɓɓun da ke kan mulki waɗanda ba naɗi ba ne, duk da sun faɗi zaɓe, sun ci gaba da riƙe muƙaman su.

Irin waɗannan sun haɗa da Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo, Gwamna Udom Emmanuel, David Umahi, Aminu Tambuwal, Bala Mohammed da Nyesom Wike.

Akwai irin su Gwamna Kayode Fayemi wanda shi ma ya na ciki, amma ya janye wa Tinubu.

Rotimi Amaechi:

Ko Buhari Zai Sake Ba Ɗan Amanar Daura Riƙon Amana?:

Rotimi Amaechi mutum ne da ya ci ribar dimokraɗiyya sosai, domin tun daga 1979 ya ake damawa da shi a jiha, har ya zama Gwamnan Jihar Ribas, tsawon shekaru takwas, daga 2007 zuwa 2015.

Daga 2015 kuma Gwamnatin Shugaba Muhammadu Buhari ta APC, ta naɗa shi Ministan Harkokin Sufuri, muƙamin da ya riƙe tsawon shekaru bakwai.

Amaechi ya ajiye muƙamin Ministan Sufuri, ya shiga siyasa, inda ya shiga takarar shugabancin ƙasa a ƙarƙashin jam’iyyar APC.

Amaechi ya gwabza zaɓen fidda gwani shi da ‘yan takara 17, bayan wasu bakwai sun janye a ranar zaɓe.

Ya yi ƙoƙari sosai, domin ya zo na biyu, amma ya samu ƙuri’u 316 kacal. Yayin da wanda ya yi nasara, Bola Tinubu ya samu ƙuri’u fiye da dubu ɗaya.

Masu fashin baƙin siyasa na fassara Amaechi da cewa ya yi tunanin zai samu ɗaurin gindi daga Fadar Shugaban Ƙasa, domin ya samu takara.

Shi kan sa Amaechi ya yi wasu abubuwa da su ka bai wa da dama mamakin cewa duk share hanyar neman takarar shugaban ƙasa ne ya sa Amaechi ya yi su.

Misali ya kai aikin gina Jami’ar Harkokin Fasahar Sufuri a Daura. Sannan kuma ya shiga, ya fita an naɗa shi sarautar gargajiya ta Ɗan Amanar Daura.

Ganin yadda Amaechi ya dira filin zaɓen fidda-gwani gwani da ƙarfin sa, kamar wani ingarman doki, ya sa mutane sun yi tunanin akwai abinda ya taka.

Sai dai kuma bayan kammala ƙidayar ƙuri’u, Amaechi ya samu 316 kaɗai.

Amaechi ya karaɗe Arewa da sauran jihohin ƙasar nan ya na neman amincewar wakilan zaɓen ‘yan takara. Amma abin mamaki, 316 kaɗai ya samu.

Shin ya aka yi gwanin rawa ya faɗi? Wasu na cewa ‘deliget-deliget’ ne su ka juya masa baya.

Wasu kuma cewa su ke yi waɗanda ya dogara da su ɗin ne su ka canja masa fuska lokacin da zaɓen ya kusanto.

Yanzu dai Amaechi ba Minista, ba takara kuma babu naira miliyan 100 da ya sayi fam.

Abin da zai fuskanta a yanzu kuma shi ne Kwamiti Binciken da Gwamna Wike ya kafa masa, inda ake zargin sa da karkatar da fiye da sama da naira biliyan 80.

Godswill Akpabio: Ko Buhari Zai Sake Rungumar Sa Bayan Ya Yi Asarar Takara, Kujerar Sanata Kuma Ya Janyo Wa APC Hana Ta Shiga Zaɓen Gwamnan Akwa Ibom?:

Wannan bayani ne kan yadda Akpabio ya sauka daga minista, ya rasa takarar shugabancin ƙasa, kuma ya rasa takarar sanatan da ya nema don rage asara.

Tsohon Ministan Bunƙasa Yankin Neja Delta, Godswill Akpabio ya ɗibga asarar takarar ƙujerar sanata, wadda ya garzaya ya yi ƙoƙarin samu bayan ya rasa kujerar ƙarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin APC.

Akpabio na cikin ‘yan takara bakwai da su ka janye wa Bola Tinubu. Shi ne ya fara janyewa, shi ya sa a zaɓen bai samu ƙuri’u ko guda ɗaya ba.

Kafin Akpabio ya shiga takarar shugaban ƙasa, inda ya ajiye aikin sa na Ministan Harkokin Bunƙasa Yankin Neja Delta.

Bayan rashin nasarar sa ne sai ya garzaya jihar su a Akwa Ibom, inda a ranar Alhamis sai APC ɓangaren sa ta shirya zaɓen fidda gwani, aka ce shi ya yi nasara.

To sai dai kuma Hukumar Zaɓe ta Ƙasa INEC ta ce ba ta amince da zaɓen fidda gwani ba wanda aka zaɓi Akpabio, domin ko wakilan INEC ba a tura domin su kalli yadda zaɓen ya gudana.

“INEC ta amince da zaɓen da aka yi wa Akinimo Udorfia tun a ranar 28 Ga Mayu, a matsayin ɗan takarar APC na Sanatan Arewa maso Yamma na Akwa Ibom.

Akpabio ya sha fama da rikici shi da tsohon Sakataren Yaɗa Labaran APC, John Akpanudoedehe.

Akpanudoedehe shi ma ya fice daga APC, inda ya koma NNPP ya samu takarar shugaban gwamnan Akwa Ibom.

Ya fice daga APC ne bayan da aka ba wani sabon-shigar APC takarar gwamna a jihar, tun bai cika kwanaki 30 da shiga jam’iyyar ba.

To shin ko yaushe ne Akpabio zai wartsake? Wataƙila idan APC ta kafa gwamnati, Tinubu ka iya saka masa da muƙamin minista a 2023.

Akpabio ya shiga rikicin ‘ba gaira ba dalili shi da tsohon Sakataren APC na Ƙasa John Akpanudoedehe. a Akwa Ibom.

Wannan rikici ya haifar da jam’iyyar ta kasa gudanar da zaɓen fidda gwani na takarar gwamna na Akwa Ibom. Lamarin da INEC ta cire sunan APC daga takarar gwamnan jihar Akwa Ibom a zaɓen 2023 mai zuwa.

Tags: AbujaAPCHausaNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Miji na na kira na ‘Yar kwatano’ tsohuwar yayi, ko gwanjo – Korafin mata a Kotu

Next Post

Ƴan bindigan da suka sace ƴan ɗaurin aure sun yi musu kuɗin goro, sun buƙaci a biya naira miliyan 145 kuɗin fansar su

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Ƴan bindigan da suka sace ƴan ɗaurin aure sun yi musu kuɗin goro, sun buƙaci a biya naira miliyan 145 kuɗin fansar su

Ƴan bindigan da suka sace ƴan ɗaurin aure sun yi musu kuɗin goro, sun buƙaci a biya naira miliyan 145 kuɗin fansar su

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Uba Sani ya yi sabbin nade-nade 27, ya nada Sani Liman shugaban ma’aikatan fadar gwamnati
  • SHUGABANCIN MAJALISAR DATTAWA: ‘A saka min wahalar da na yi wa APC, a ba ni shugabancin Majalisar Dattawa’ – Osita Izunaso
  • SHUGABANCIN MAJALISA: ‘Ba zan janye wa kowa ba, amma na ‘jone’ da guruf ɗin Abdul’aziz Yari’ – Orji Kalu
  • Kamfanin mai na kasa ya kara kudin litar mai daga N189 zuwa N537
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Peter Obi ya nemi kotu ta ɗage sauraren shari’ar da ya maka Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.