Yayin da aka shiga ranar fara taron zaɓen fidda gwani na masu takarar shugaban ƙasa a APC, a yanzi dai kan gwamnoni da na Kwamitin Gudanarwa na APC ya haɗu, inda su ka fitar da ‘yan takara 5 daga cikin 22 masu nema, su ka yi fatali da 17.
Tuni dai aka miƙa wa Shugaba Muhammadu Buhari sunayen mutane biyar ɗin da aka amince cewa a cikin su ne za’a fitar da ɗan takara.
Da ya ke zantawa a ranar Alhamis da safe, Gwamna Simon Lalong na Jihar Filato ya ce sun aika wa Buhari da sunayen Bola Tinubu, Kayode Fayemi wanda a yanzu shi ne Gwamnan Jihar Ekiti, David Umahi Gwamnan Ebonyi, tsohon Ministan Sufuri Rotimi Amaechi da kuma Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo.
Lalong ya ce Buhari ya duba sunayen kuma ya ce duk sun cancanta.
Ya ce sun fitar da sunaye 5 ne saboda ba zai yiwu a yafi zaɓen fidda-gwani da sunaye rututu ba.
Sai dai kuma ya ce duk da an fitar da sunayen, ba a hana duk wanda aka yi fatali da sunan sa ya fito zaɓen fidda-gwanin ba.
Idan ba a manta ba, Gwamnan Jigawa Badaru Abubakar ya ce har yanzu Buhari bai yanke shawarar miƙa takara ga ɗan kudu kai-tsaye ba.
Gwamna Abubakar Badaru na Jigawa ya ce har yanzu gwamnonin APC na Arewa na jiran Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana matsayar sa kan miƙa takarar shugaban ƙasa ga ɗan kudu kai-tsaye.
Badaru ya bayyana haka a cikin wata tattaunawar da ya yi da BBC Hausa a ranar Lahadi.
A ranar Asabar ce dai Gwamnonin APC na Arewa da masu faɗa-a-ji na jam’iyyar daga Arewa, su ka amince mulki ya koma kudu a zaɓen 2023. Wato dai APC za ta tsayar da ɗan takara kenan daga kudu.
Badaru wanda shi ma ya na cikin ‘yan takarar shugaban ƙasa, ya ce har yanzu Buhari bai bayyana matsayar sa a kan amincewa ko rashin amincewa da hakan ba.
Badaru ya ce maganar gwamnoni Arewa sun amince, bai tayi ne su ka miƙa, ba a kai ga daddalewa ba tukunna.
Badaru ya ce ya yi mamakin da ya ji “wai an raba takardar bayan taro mai ɗauke da sa hannun mutane, wadda a maganar gaskiya ba haka abin ya ke ba.
“Mu tayi ne mu ka miƙa wa Baba Buhari, idan ya ga hakan ne mafita kuma ya amince, shikenan, sai a yi hakan. Idan kuma bai amince ba, sai mu ci gaba a kan tsarin da mu ke. Amma dai mu gwamnonin Arewa mu ka goyon bayan duk wata matsaya da Buhari ya bijiro da ita.”
Ya ce Gwamnonin Arewa sun wakilta Gwamna Atiku Bagudu na Kebbi da Simon Lalong na Filato da Abdullahi Sule na Nasarawa su je su sanar wa Shugaba Buhari cewa sun yarda duk ɗan Arewa mai takara a APC, to ya janye a bar wa ‘yan kudu su fito da ɗan takara a cikin su.
“Gaskiya ne Gwamnonin Arewa kamar su 11, ciki har da Ni mun tattauna wannan batu, sannan mu ka aika wa Shugaba Buhari cewa mun yi la’akari da halin da ake ciki, saboda haka mun yarda a bai wa ‘yan kudi takarar shugaban ƙasa a ƙarƙashin APC.”
“Maganar janyewa ta kuwa, ba za ni yi gaggawar janyewa ba, har sai na ji matsayar da Shugaba Buhari ya fitar.”
Wato dai kenan har yanzu dukkan ‘yan takarar 23 kowa na ciki, ko ɗaya bai janye ba.