Ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana dalilan da su ka sa ya ɗauki Gwamnan Jihar Delta Ifeanyi Okowa ya yi masa takarar mataimakin gwamna a zaɓen 2023.
“Na yanke shawarar zaɓar mataimakin takara ne wanda tilas ya san irin halin taɓarɓarewa da lalacewa da rugu-rugun da gwamnatin APC ta yi wa wannan ƙasar.” Inji Atiku.
Atiku Abubakar ya zaɓi Ifeanyi Okowa domin kamar yadda ya ce wanda zai ɗauka tilas zai kasance ya na da masaniyar muhimmancin ilmi a cigaban zamani cikin al’umma, ta yadda za mu shirya matasa su riƙa yin gogayya da sauran ƙasashen duniya a zamanance.”
Sauran dalilan da ya lissafa sun haɗa da wanda ya ke da shauƙin ganin an ƙara haɗa kan Najeriya, kuma wanda zai taimaka masa a samu wannan nasarar.
Atiku ya nuna farin cikin yadda aka gudanar da zaɓen fidda gwani lafiya, kuma ya gode wa sauran ‘yan takarar da ya kayar, tare da sake neman haɗin kan su domin a tafi tare har a kai ga nasara.
“Kuma ina farin ciki da alfaharin fatan cewa idan na samu masarar zama shugaban ƙasa, to mataimaki na ne zai gaje ni. Don haka ya zauna da shirin shi ma Shugaba ne mai jiran gado.
“Kuma mataimakin takara ta zai kasance wanda a shirye ya ke ya taimake ni mu kawo ƙarshen matsalar tsaro a faɗin ƙasar nan.”
Atiku ya ce tilas mataimakin sa zai kasance wanda zai taya shi dawo da ɗimbin masu zuba jari daga waje waɗanda su ka gudu daga ƙasar nan, yayin da gwamnatin APC ke barci har ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga masu ƙaryar su makiyaya ne su ka addabi ƙasar nan, da manoma da makiyayan ainihi.
Atiku ya ce ya saba ɗaukar matsayi mai wahala sosai. Don haka a yanzu ma sai da ya tsaya ya darje, bayan ya tuntuɓi manyan masu ruwa da tsaki sosai, sai ya ɗauki Ifeanyi Okowa.
Atiku ya ce a yanzu ba lokacin tsayawa surutai ba ne, jan aikin da ke gaban su shi ne tabbatar da cewa an yi nasara a zaɓen 2023.