• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

    ABUJA: Kotu ta daure wasu ‘yan mata biyu saboda yawon gulmace-gulmace a unguwa

    Kotu ta tsare matar da aka kama tana madigo da ‘yar shekara 8 a Kaduna

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Mahukunta a Abuja sun kama ƴan iskan gari mutum 400 da motoci 50 da suka karya doka

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    Tinubu ya naɗa tsohon ministan Abuja, Modibbo, Kakanda, Baba-Ahmed mashawarta a ofishin mataimakin shugaban kasa

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun kama tsohon da ya yi wa ‘yar shekara hudu fyade a Katsina

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SABON GARGAƊIN INEC GA JAM’IYYU: Ba za mu ƙara maku wa’adin zaɓen fidda gwanaye ba

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 12, 2022
in Rahotanni
0
ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Dalla-dallar yadda INEC ta ƙarfafa matakan tsaron gano katin rajistar bogi

Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta nanata matsayin ta cewa ba za ta ƙara wa’adin da ta tsara na gudanar da zaɓuɓɓukan fitar da gwanaye na jam’iyyun siyasa ba.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, shi ne ya bayyana haka a wajen taro karo na biyu da ya kan yi da jam’iyyun siyasa a duk wata hurhuɗu na shekarar 2022, wanda aka yi a ranar Litinin a Abuja.

A cewar sa, akwai ayyuka da dama da masu alaƙa da juna a kan batun wa’adin zaɓuɓɓukan waɗanda tilas ne a aiwatar da su.

Saboda haka, a cewar sa, duk wani canji da za a yi wa wa’adin zai iya shafar sauran ayyukan ta yadda ba a so, kuma yin hakan zai kawo matsaloli ga jam’iyyun da ita kan ta hukumar.

Yakubu ya ce, “Lokacin da jam’iyyun su ka ware domin yin zaɓuɓɓukan fidda gwanayen ya fara ne daga ranar 4 ga Afrilu, 2022 kuma zai ƙare kwanaki 24 daga yau ɗin nan, wato a ranar 3 ga Yuni, 2022.

“Sau biyu a cikin mako biyu da su ka gabata, sai da hukumar ta fito ta tunatar da jam’iyyun siyasa batun muhimmancin da ke akwai na tsayawa sau da ƙafa kan zaɓuɓɓukan su na fidda gwanaye. Ina ƙara nanata matsayin hukumar na cewa ba za a sauya wa’adin da aka tsara ba.

“Akwai ayyuka sosai masu alaƙa da juna waɗanda su ka shafi wa’adin, waɗanda tilas ne a aiwatar da su. Duk wani sauyi da za a yi na ƙara tsawon wa’adin don wani aiki ƙwaya ɗaya zai shafi sauran ayyukan kuma ya jawo matsaloli ga jam’iyyun siyasar da ita kan ta hukumar. A ƙarshe hakan zai haifar da ƙarin manyan matsaloli fiye da abin da aka so magancewa da ƙarin wa’adin.

“Don haka, wannan hukuma ba za ta sauya wa’adin ba. Idan mu ka ci gaba da aiki tare, za mu iya tafiya a kan lokacin wa’adin wajen gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwani cikin aminci da dimokiraɗiyya don zaɓen ‘yan takara na mazaɓu 1,491 waɗanda za a yi wa zaɓe a ranakun 25 ga Fabrairu da 11 ga Maris, 2023.”

Shugaban ya bayyana cewa hukumar tasa ta shirya wani kundi wanda zai zama jagora ga jam’iyyun siyasar wajen gudanar da zaɓuɓɓukan su na fidda gwanaye da fitar da ‘yan takarar zaɓe.

Ya ce: “A bisa tsarin yin aiki tare don bin ƙa’idojin da doka ta tanada, wannan hukuma ta shirya wani kundi da zai yi wa jam’iyyun siyasa jagora wajen gudanar da zaɓuɓɓukan fitar da gwanaye tare da tsayar da ‘yan takarar su na zaɓe, wanda ya haɗa da jerin takardun da ake buƙata don kammala aikin tsayar da ɗan takara cikin nasara.

“Kundin ya na daga cikin ƙunshin takardun da mu ka ba ku na wannan taron. Haka kuma, hukumar ta shirya kalandar lokutan zaɓuɓɓukan fidda gwanaye na muƙaman shugaban ƙasa, gwamna, da majalisun tarayya da jihohi bisa shawarwarin da jam’iyyun siyasa su ka kawo ya zuwa ranar Juma’a, 6 ga Mayu, 2022. Ita ma wannan takarda ta na cikin ƙunshin takardun da mu ka ba ku domin wannan taron.”

Shugaban ya yi kira ga jam’iyyun da su rungumi kowa da kowa wajen gudanar da zaɓe ta hanyar tabbatar da cewa sun ba mata da matasa da naƙasassu damarmaki sosai.

A cewar sa, wannan ce kaɗai hanyar da za su bi su ba jama’ar ƙasa tabbacin sadaukarwar su ga mulki mai nagarta, ba kawai su tsaya a maganar fatar baki ba.

Ya ce: “A yayin da ku ke gudanar da zaɓuɓɓukan fidda gwanayen tare da tsaida ‘yan takarar ku na zaɓe, yanzu ne lokacin da ya dace mu tuna maku sadaukarwar ku ga inganta tafiya tare da kowa da kowa a harkar zaɓe. Mata da matasa da naƙasassu sun jima su na so a riƙa ba su babban wakilci, musamman a muƙaman zaɓe.

“Don tabbatar wa da jama’ar ƙasa cewa ba kawai maganar fatar baki ake yi kan wannan batu ba, ya kamata jam’iyyun siyasa su ƙarfafa wa dukkan waɗanda ba a cika sanya su cikin harkar zaɓe ba gwiwa wajen shiga a dama da su a matsayin ‘yan takara a zaɓe. Wannan kaɗai ce hanyar da za mu bi mu sauya abin da ke faruwa na rashin isasshen wakilci na wannan muhimmin sashe na al’umma, musamnan ma a zaɓaɓɓun majalisu da kuma sha’anin mulki baki ɗayan sa a ƙasar mu.”

Yakubu ya tunatar da masu ruwa da tsaki a zaɓuɓɓukan gwamna da ke tafe a jihohin Ekiti da Osun kan buƙatar da ke akwai ta jam’iyyun siyasa su zo su ga samfur na kayan aikin zaɓen da hukumar ta tanadar masu.

Ya ce, “Idan mun juya ga wasu zaɓuɓɓukan, ina so in tuna maku cewa za a yi zaɓen gwamnan Jihar Ekiti a wata mai zuwa, a ranar Asabar, 18 ga Yuni, 2022, yayin da za a yi zaɓen gwamnan Jihar Osun nan da wata biyu, a ranar Asabar, 16 ga Yuli, 2022.

“Sashe na 42 na Dokar Zaɓe ta 2022 ya buƙaci hukumar da ta gayyato jam’iyyun siyasa domin su duba samfur na kayan aikin zaɓen aƙalla kwana 20 kafin ranar zaɓen. Don kiyaye wannan dokar, mun gayyato dukkan jam’iyyun siyasa da su ke da ‘yan takara a zaɓen gwamnan Jihar Ekiti domin su duba samfur na kayan aikin a ranar Laraba, 18 ga Mayu, 2022 a ɗakin taro na hukumar da ke Abuja da ƙarfe 11:00 na safe.”

Shugaban na INEC ya yi kira ga jam’iyyun da su tabbatar da sun yi yaƙin neman zaɓe mai tsafta ba tare da wata hatsaniya ko tada hankali ba.

Ya ce, “A yayin da ku ke kamnala zaɓuɓɓukan ku na fidda gwanaye tare da shirya wa zaɓuɓɓukan cike gurbi da manyan zaɓuɓɓuka, ina kira a gare ku da ku tabbatar da kun yi yaƙin neman zaɓe mai tsafta ba tare da wata hatsaniya ko tada hankali ba. Don yin hakan, tsayawa kan dimokiraɗiyyar cikin gida ya na da muhimmanci.

“Abin baƙin ciki, yawan ƙararrakin da wasu ‘yan jam’iyya su ka kai junan su kan zaɓuɓɓukan fidda gwani ya zuwa yanzu sun haura 807 da aka samu kafin Babban Zaɓen 2019 inda masu ƙarar su ka maƙalo har da wannan hukuma.

“Bugu da ƙari, duk dai mun san yanayin tsaro da ake ciki a ƙasar nan ya isa babbar matsala. Kada da gangan ko ba da sani ba ku ƙara hargitsa halin da ake ciki ta hanyar halayya ta tashin-tashina ta membobin ku da magoya bayan ku a lokacin zaɓuɓɓukan fidda gwanaye da babban zaɓe.

“A yayin da za mu fara taron mu na biyu daga cikin tarurruka huɗu da za mu yi a bana, ina ba shugabannin jam’iyya tabbacin cewa a yayin da hukuma ba za ta sa hannu a zaɓen ku ba, za dai ta tsaya ƙyam, za mu ci gaba da yin aiki da jam’iyyun siyasa a matsayin su na manyan masu ruwa da tsaki domin alfanun ƙasar mu.”

Tags: AbujaAPCINECLabaraiNewsPDPPREMIUM TIMES
Previous Post

Duk wani mai takarar kujerar siyasa da na naɗa a gwamnati na ya ajiye aiki daga yau zuwa 16 ga Mayu -Buhari

Next Post

TAKARAR GWAMNAN NEJA 2023: Idan na yi nasara zan yi aiki tuƙuru wajen bunƙasa Jihar Neja – Malagi

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
TAKARAR GWAMNAN NEJA 2023: Idan na yi nasara zan yi aiki tuƙuru wajen bunƙasa Jihar Neja – Malagi

TAKARAR GWAMNAN NEJA 2023: Idan na yi nasara zan yi aiki tuƙuru wajen bunƙasa Jihar Neja – Malagi

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Wike ya soke lasisin mallakar filayen wasu jigajigan Najeriya ciki har da Peter Obi
  • Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa
  • Kotu ta bada belin mutumin da ke zargin wani da sace masa ‘gaba’
  • Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun
  • DOKAR HANA ZIRGA-ZIRGA: Garƙame mu da aka yi a Kano ya jawo mana hasara a Kasuwa, an jefa mutane ciki takura

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.