Gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai ya gargadi jami’an tsaro da su maida hankali matuka domin alamu sun nuna cewa Boko Haram da ‘Yan kungiyar Ansaru sun darkako jihar Kaduna.
” Muddun ba a maida hankali wajen kawo karshen wannan matsala ba tunda wuri za a afka cikin matsanancin halin rashin tsaro a yankin Arewa Maso Yamma da zai fi wanda aka yi fama da shi a Arewa Maso Gabas domin maganin gaskiya shine akwai karancin jami’an tsaro da ake fama da shi a kasar nan.
El-Rufai ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen mika rahoton bayanai kan tsaron jihar na wata wata da ma’aikatar tsaron jihar karkashin Kwamishina Samuel Aruwan ta yi.
” Baya ga darkakowar Boko Haram jihar Kaduna, a yanzu haka sun mamaye yankunan kananan hukumomin birnin Gwari da Chikun, an samu yawaitar dashe-dashen nakiyoyi a sassan jihar da dama. Muna wa Allah godiya jami’an tsaron jihar sun gano su suna kuma ciccire su.
” Baya ga nakiyoyi da ake ta cirewa da aka daddasa, shaye-shayen muggan kwayoyi ya yawaita a jihar Kaduna yanzu. Abinda gwamnati ke kokarin yi yanzu shine a kirkiro dokar da zai ba hukumar tsara birane ta jihar damar kwace gini da rusa duk wani shagon da aka samu yana saida muggan kwayoyi. Ina so in tabbatar muku cewa abin fa yayi munin gaske.
” Dole sai an kawo karshen ta’ammali da muggan kwayoyi da saida su domin sune yan ta’adda ke sha idan za su aikata ayyukan ta’addancin su.
A karshe gwamna El-Rufai ya yaba wa jami’an tsaro dake aiki a jihar bisa kokarin da suke yi wajen ganin ana samun nasara wajen harkar tsaro a jihar. Sannan kuma ya ce jami’an sa kai da gwamnati ta dauka suna taimakawa wajen harkar tsaro a jihar.
Discussion about this post