Shugaba Muhammadu Buhari da Ministan Shari’a Abubakar Malami, sun garzaya Kotun Ƙoli, su na neman a yi masu fassara da sharhin ma’anar wani sashe na Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022.
Buhari da Malami sun shigar da ƙarar tun a ranar 29 Ga Afrilu, inda su ka maka Majalisar Dattawa da Majalisar Tarayya kotu.
Sashe na 84(12) na Sabuwar Dokar Zaɓe dai ya shiga harankazamar ja-in-ja a Najeriya, tun bayan da Shugaba Muhammadu Buhari ya sa wa Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022 hannu cikin watan Fabrairu.
Jim kaɗan bayan Buhari ya sa wa ƙudirin dokar hannu ta zama doka, ya roƙi Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa cewa su soke wancan sashe da ake ta tankiya a kan sa, amma su ka yi ƙememe, su ka ƙi goge shi.
Abin Da Sashe Na 84(12) Ya Ƙunsa:
“An haramta wa mai riƙe da muƙamin siyasa ko muƙamin gwamnati ko shugabancin jam’iyya yin zaɓe a matsayin wakilin masu zaɓen ‘yan takara. Kuma ba a yarda a zaɓe shi ba, sai da idan ya ajiye muƙamin sa.”
Idan ba a manta ba, watanni biyu da su ka gabata, Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia a Jihar Abiya ta soke wannan sashe na 84(12), bisa dalilin cewa ya ci karo da Kundin Dokokin Najeriya.
Azarɓaɓin Minista Malami:
Minista Malami ya yi azarɓaɓin cewa zai soke dokar domin bin umarnin Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia. Sai dai kuma a lokacin ya na da kwaɗayin takarar gwamna a jihar Kebbi.
Kafin Malami ya soke dokar, sai Kotun Ƙoli ta yi gaggawar soke hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia ta zartas. Kotun Ɗaukaka Ƙara ta ce kada a sake a soke dokar.
Ganin haka ne a yanzu Buhari da Malami su ka dira Kotun Ƙoli, domin a san matsayar wannan Sashe na 84(12) da ke cikin Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2023.
A makon jiya ne Premium Times ta buga labarin yadda Majalisar Tarayya Ta Bi Ra’ayin Majalisar Dattawa, Sun Yi Wa Sashe Na 84 (8) Na Sabuwar Dokar Zaɓe Kwaskwarima:
Majalisar Tarayya ta amince tare da aikawa da kwaskwarimar da su ka yi wa Sabuwar Dokar Zaɓe Sashe na 84 (8) na 2022, ta yadda wakilan zaɓen ‘yan takara masu riƙe da muƙaman gwamnati za su samu damar yin zaɓen fidda-gwani, taron gangami da tarukan jam’iyya.
Majalisar Tarayya ta yi wa sabuwar dokar kwaskwarima ce bayan ta yi la’akari da Kudirin da Shugaban Kwamitin Majalisa Abubakar Fulata ya gabatar a ranar Laraba, a Abuja.
Kudirin dai mai suna, “Kudirin Yin Kwaskwarima Ga Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022 Mai Lamba 13”, ya bayar da dama ga wakilan jam’iyya masu riƙe da muƙaman gwamnati su yi zaɓe a lokacin zaɓukan fidda-gwanin ‘yan takarar jam’iyyu.
Idan an tuna, Sabuwar Dokar Zaɓe wadda Shugaba Muhammadu Buhari ya sa wa hannu cikin watan Fabrairu 2022, ta haramta wa masu riƙe da muƙaman gwamnati su yi zaɓen fidda gwani.
Su Wane Ne Masu Riƙe Da Muƙamai?:
Sun haɗa da: Kansilolin mazaɓu da ke ƙananan hukumomi, shugabannin ƙananan hukumomi da mataimakan su, shugabannin jam’iyyu na ƙananan hukumomi 774, ‘yan majalisar dokokin jihohi da ‘yan majalisar tarayya.
Sauran sun haɗa da: Gwamnoni, mataimakan gwamnoni, shugaban ƙasa da mataimakin sa, Shugabannin Majalisar Gudanarwar Jam’iyya, shugabannin jam’iyya na jihohi, na ƙananan hukumomi da sakatarorin su.
Wannan sabuwar doka da aka yi wa kwaskwarima za ta bai wa waɗannan da aka lissafa a sama su yi zaɓen ‘yan takara a zaɓen fidda gwani.
Idan ba a manta ba, Majalisar Dattawa ta amince da wannan kwaskwarima tun a ranar 10 ga Mayu, 2022.
A farkon shekarar nan PREMIUM TIMES Hausa ta riƙa kawo kwatagwangwamar da ta dabaibaye wannan sabuwar doka. Har ta kai an bada wani rahoton da babban lauya Femi Falana ya zargi Ministan Shari’a Abubakar Malami da yin surunkutumi cikin sha’anin hukuncin kotu.
‘Yadda Ministan Shari’a Malami ya damalmala hukuncin kotu a kan Dokar Zaɓe’ -Femi Falana:
Babban Lauya mai rajin kare haƙƙi da ‘yancin jama’a Femi Falana ya zargi Ministan Shari’a Abubakar Malami da damalmala Babbar Kotun Tarayya ta yadda ta bayar da hukunci baddalalle mai cike da tarnaƙi akan matsayar sashe na 84(12) na Sabuwar Dokar Zaɓe ta 2022.
Falana ya ce Malami ya yi bakam, ya nuna kamar bai ma san akwai wani hukunci ko umarnin kotu wanda na Kotun Tarayya wanda ya haramta masa yin katsalandan a kan dokar. Amma sai ya jajirce cewa shi sai ya yi amfani da umarnin Babbar Kotun Umuahia, wadda ta bayar da umarnin a soke wannan sashen ɗungurugum.
Falana wanda babban lauya ne (SAN), ya fitar da sanarwa inda ya bayar da cikakken bayanin yadda Manyan Kotunan Tarayya guda uku suka bayar da mabanbantan hukunce-hukunce. Daga nan Falana ya ɗora laifin gaba ɗaya a kan Ministan Shari’a Malami.
“Don haka sai Falana ya ce ya kamata Malami ya sani cewa ba fa zai iya yin yadda ya ga dama ba, ta hanyar bin umarnin da ya ga dama, kuma ya bijire wa wadda ya gada dama.
“Sannan kuma babu sauran wata jikara ko tantama, tabbas Ministan Shari’a ya damalmala hukuncin Babbar Kotun Tarayya har ta bayar da baddalallun hukunce-hukunce a kan sashe na 84(12) na Dokar Zaɓe ta 2022.” Inji Falana.
Malami Ko ‘Malam Karkata’: Yadda Minista Malami Ya Sa Kotunan Tarayya Su Ka Bayar Da Mabambantan Hukunce-hukunce A Shari’a Ɗaya -Femi Falana:
Idan za a tuna, a ranar 18 Ga Maris, Kotun Tarayya ta Umuahia a Jihar Abia ya soke Sabuwar Dokar Zaɓe Sashe na 84(12), wanda ta ce ya ci karo da wani sashe na Dokar Ƙasa. Wannan sokewa dai ya kasance an yi abin da Shugaba Muhammadu Buhari ke so kenan, wato a soke dokar.
Sashen dai ya haramta wa masu riƙe da muƙamai na siyasa su shiga zaɓe a matsayin wakilan ‘deliget’ yayin gangamin zaɓen shugabannin jam’iyya da sauran su.
Mai Shari’a Evelyn Anyadike ta ce wannan sashe na doka da ta soke, ba shi da hurumi a cikin kundin dokokin Najeriya, haramtacce ne, ba shi ma da wani amfani.”
Daga nan ta umarci Ministan Shari’a kuma Antoni Janar ya goge dokar a cikin daftarin dokokin Najeriya. Wato aka ce ya shafe Sashe na 84(12) na Dokokin Zaɓe na 2022.
Ta ce dokar ta ci karo da wani sashe wanda ya bai wa masu riƙe da muƙamai damar tsayawa takara, amma su ajiye muƙaman su ana saura kwana 30 kafin zaɓe.
Sai dai kuma lauyoyi da dama sun la’anci wannan matsaya ta soke wani sashe na doka.
Da ya ke a ƙarar da aka shigar tun da fari, har da Abubakar Malami aka gurfanar. Shi kuma Malami ya nuna shauƙin son ya soke Sabuwar Dokar.
Ko ba komai dai soke dokar zai taimaki malami a matsayin sa wanda zai tsaya takarar gwamnan Jihar Kebbi a zaɓen 2023.
Falana ya ce Malami ya wulaƙanta ofishin sa da muƙamin sa, saboda ya tafi ‘ya na shawagin-dibak-kaɗe’, don kawai ya sami wasu hukunce-hukunce da zai rataya a wuya, don ya soke dokar zaɓe ta Sashe na 82(12).
Idan kuma ba a manta ba, a ranar 8 Ga Maris, 2022 Mai Shari’a Inyang Ekwo na Babbar Kotun Tarayya ya bayar da hukunci a kan wata ƙara da PDP ta shigar a kan Dokar Zaɓe, tunda ta zama doka, cewa kada a kuskura wani Ministan Shari’a ya taɓa Dokar Zaɓe ko ya soke ta kwata-kwata.
Ba Abubakar Malami kaɗai kotun ta yi wa gargaɗin ba, har da Shugaba Muhammadu Buhari sai da kotun ta ce ko shi bai isa ya taɓa Dokar Zaɓe ta 2022 ba. Haka nan kuma ta gargaɗi Majalisar Tarayya da ta Dattawa.
Amma abin mamaki, kwanaki 10 bayan wannan hukuncin, yayin da aka taɓo batun a Babbar Kotun Tarayya ta Umuahia, sai labari ya sha bamban, kotun ta bayar da umarni ga Minista Malami cewa ya soke dokar.
A kan haka ne Falana ya nuna ɓacin rai ya ce Malami ya yi wa fannin shari’a tuƙin ganganci, ta hanyar ƙin sanar da Babbar Kotun Umuahia cewa akwai hukunce-hukunce biyu a baya waɗanda su ka hana a taɓa sabuwar dokar ko a soke ta.
Discussion about this post