• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Hasalallun Sanatocin APCn da su ka faɗi zaɓen fidda-gwani sun gana da Buhari

    Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

    INEC ba za ta rufe rajistar zaɓen 2023 a ƙarshen Yuni ba – Farfesa Yakubu

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Buhari ya rantsar da sabon Cif Joji na riƙo

    Teacher

    Gwamnati ta umarci makarantu su fara amfani da Tsarin Ƙara wa Malamai Shekarun Ritaya

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    ‘Yan sanda sun damke dan shekara 30 din da ya nemi yi wa dattijiya mai shekaru 75 fyade

    Petrol Tankers

    ƊAN KUKA MAI JA WA UWAR SA JIFA: Ƙungiyar IPMAN ta ce ba za ta iya ci gaba da sayar da fetur a garuruwan yankin Igbo ba

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

FIDDA-GWANIN SHUGABAN ƘASA 2023: Yadda gwamnoni ke baki-biyu tsakanin su ‘yan naci, ‘yan mai-rabo-ka-ɗauka da ‘yan idan-ta-yi-ruwa-rijiya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
May 23, 2022
in Babban Labari
0
FIDDA-GWANIN SHUGABAN ƘASA 2023: Yadda gwamnoni ke baki-biyu tsakanin su ‘yan naci, ‘yan mai-rabo-ka-ɗauka da ‘yan idan-ta-yi-ruwa-rijiya

Yayin da ranakun zaɓen-fidda-gwanin jam’iyyun siyasa don fitar da ɗan takarar shugaban ƙasa ke ƙaratowa, tabbas wasu ‘yan takarar za su janye ne a cikin wannan makon, ganin yadda gaba-ɗayan karafkiya da cukumurɗar siyasar ta koma a cikin gida.

A ƙarshen makon nan ne APC da PDP za su yi zaɓen su na fidda-gwanin ɗan takarar shugaban ƙasa a Abuja.

PDP na da ‘yan takara 15, ita kuwa APC na da 25.

Da alamu a PDP ɓangaren kudancin ƙasar nan, sun ɗauki matsaya ɗaya, tun bayan da jam’iyyar ta ce kowa ma ya fito ko daga wane yanki ya ke, babu maganar tsarin karɓa-karɓa.

A APC kuwa mutum 28 ya sayi fam na takarar Shugaban Ƙasa. Amma mutum uku ba su maida fam ɗin ba, wanda aka riƙa sayarwa Naira miliyan 100.

Minista Chris Ngige, Gwamnan CBN Godwin Emefiele da Minista Timipre Sylva duk ba su mayar da fam ɗin da aka ce an saya a madadin su ba.

Sai dai kuma akwai ɗaure kai a jawabin. Saboda Shugaban Bankin Bunƙasa Afrika Akinwunmi Adesina bai je ya ɗauki fam ɗin sa ba. Shi kuma tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan bai tantance barcin makaho ba har yanzu.

Idan Akinwunmi ya nesanta kan sa, Jonathan ma ya noƙe, kenan saura ‘yan takara 23 a APC.

Sai dai kuma bisa dukkan alamu, akwai yiwuwar ‘yan takara da dama za su janye su bar wa wasu, domin har sun fara ƙulla ƙawancen yin hakan.

Batun Cimma Daidaiton Tsayar Da Ɗan Takara Ɗaya Kudu Maso Yamma:

Yayin da Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo ke magana da wakilan zaɓen ‘yan takarar shugaban ƙasa a Osogbo, babban birnin Jihar Osun, ya ce nan ba da daɗewa ba yankin Kudu-maso-yamma zai fitar da ɗan takara ɗaya, ta hanyar cimma matsaya ko yarjejeniya.

Daga yankin dai akwai Osinbajo, Bola Tinubu, Kayode Fayemi, Ibekunle Amosun, Dimeji Bankole da Tunde Bakare duk daga APC.

Dama kuma tun a farkon Mayu ne sun yi irin wannan taron a yankin.

A PDP kuwa, ‘yan takara daga Kudu maso Gabas sun yi taron ƙoƙarin cimma yarjejeniya, yayin da Arewa ƙoƙarin hakan ya gamu da cikas, lokacin da wata ƙungiyar dattawa ta ce ta tsayar da Bukola Saraki shi da Gwamna Bala Mohammed na Bauchi.

Atiku Zai Sake Jaraba Sa’a Shi Da Peter Obi?:

A wannan makon kuwa lamarin zai sauya baki ɗaya. Saboda ana raɗe-raɗin cewa Atiku zai sake ɗaukar Peter Obi ya yi takarar Mataimakin shugaban ƙasa ga Atikun, kamar dai yadda su ka yi a 2019.

Sai dai kuma wata majiya na cewa Atiku na ganawa da gwamnonin PDP, waɗanda idan har Atikun ya yi nasara a zaɓen fidda gwani, to ya ɗauki mataimaki daga cikin gwamnonin.

Yunƙurin ‘Yan Takarar Ƙananan Jam’iyyu:

Mutum bakwai ya sayi fam na jam’iyyar ADC kan kuɗi Naira miliyan 25. Daga cikin su akwai Kingsley Moghalu, toshon Mataimakin Gwamnan Babban Bankin CBN, wanda ko a zaɓen 2019 sai da ya yi takara a ƙarƙashin YPP.

Fafarniya Da Nacin Da Sanata Ahmad Lawan Ke Yi Kafin Zaɓen Fidda-gwani:

Sanata Ahmad Lawan ne na ƙarshen fitowa takara da sayen fam a APC. Da ya ke jawabi a Daura, Lawan ya ce turo shi aka yi domin ya tsaya takarar shugaban ƙasa.

Ya ce abokai da abokan arziki ne su ka matsa masa lambar fitowa takara.

A hakan kuma ya ce tabbas ya cancanci fitowa, kuma ya na da laƙanin iya yi wa Najeriya kyakkyawan riƙon shugabanci.

Yaƙin Neman Zaɓe Sai Mai Jirgin Rangadin Ƙasa:

Idan ɗan takarar shugaban ƙasa ba shi da jirgin kan sa, wanda zai riƙa zirga-zirgar ziyarar jihohi ya na sagarabtun nan haɗin kan masu zaɓen ‘yan takarar shugaban ƙasa, to kuwa tilas sai ya tanaji jirgin da zai ɗauka shata.

Saboda kusan dukkan manyan ‘yan takarar sun ƙaurace wa zirga-zirga kan titunan ƙasar nan, bisa alama saboda matsalar tsaro.

Wani rahoto ya nuna yadda wasu gwamnoni 9 su ka kashe maƙudan miliyoyin kuɗaɗe domin gararambar neman kujerar shugaban ƙasa, tun ma kafin zaɓen fidda-gwani.

Gwamnonin da ke takara a ƙarƙashin APC da PDP sun haɗa da Nyesom Wike na Ribas, Kayode Fayemi na Ekiti, Aminu Tambuwal na Sokoto, Bala Mohammed na Bauchi, Emmanual Udom na Akwa Ibom, Ben Ayade na Cross River, Dave Umahi na Ebonyi, Mohammed Badaru na Jigawa da Yahaya Bello na Kogi.

‘Ga Gani, Ka Gani Ƙwalelen Ka’: Yadda Gwamnoni Ke Wa ‘Yan Takarar Shugaban Ƙasa Ƙwalelen ‘Daligets’:

A makon jiya Jihar Kaduna ta ce masu zaɓen ‘yan takarar jihar su na goyon bayan Bola Tinubu.

Amma kuma kwana biyu sai Gwamna El-Rufai ya ce su jihar Kaduna za su zaɓi Rotimi Amaechi ne.

Tsakanin Amaechi Da Tinubu: Wa Wakilan Jigawa Za Su Zaɓa?

Yadda Tinubu Ya Taimake Ni Na Zama Gwamnan Jigawa -Badaru:

Gwamna Abubakar Badaru na Jihar Jigawa ya yi bitar tunin yadda tsohon Gwamnan Jihar Legas, Bola Tinubu ya taimaka aka kafa jam’iyyar APC, wadda albarkacin ta ne shi Badaru ya zama gwamna a Jigawa cikin 2015.

Da ya ke jawabi a gaban wakilan zaɓen ‘yan takarar shugaban ƙasa na jihar Jigawa a ranar Juma’a a gaban Tinubu, Badaru ya ce da taimakon da Tinubu ya yi wa jam’iyyar ne ta kai shi ga samun nasara a Jihar Jigawa, cikin 2015.

“Mun nemi jam’iyyar da za mu shiga takarar gwamna cikin 2011. Asiwaju Bola Tinubu ya samar min jam’iyya. Na shiga zaɓe, na zo na biyu.”

Badaru ya ce duk da ya haɗu da ƙalubale a 2011, amma dai goyon bayan da ya samu a lokacin ne ya ƙara masa ƙaimin samun nasara a zaɓen 2015.

Badaru ya ce ya na cikin mutane ƙalilan waɗanda za su iya shiga har cikin ɗakin kwanan Tinubu, su tashe shi daga barci.

Ya ce akwai alaƙa mai ƙarfi da shaƙuwa ta ƙut-da-ƙut a tsakanin sa da Tinubu.

Ya ce su a Jigawa ‘yan ga-ni-kashe-nin Shugaba Buhari ne. Kuma za su iya yin duk abin da Buhari ya ce su yi. “Amma fa in dai son Buhari ne a ƙasar nan, to ba wanda ya kai Tinubu son Buhari.”

Ya ce duk wasu surutai da ake yi kan titi, na shirme ne, domin babu wanda ya san iyakar alaƙar da ke tsakanin Buhari da TInubu.

Jawabin Tinubu A Jigawa: Zan Kayar Da Badarun Ku A Wurin Zaɓen Fidda Gwani, Ku Zaɓe Ni Kawai:

Da ya ke jawabi, Tinubu ya ce duk da ya san Badaru ya fito takara, to zai kayar da shi a zaɓen fidda gwani. Don haka su zaɓe shi kawai.

Wannan furuci na sa ya birge ɗimbin jama’ar da ke wurin ana ta kuwwa da tafi. Wasu na “Sai Asiwajun Legas”. Sai Jagaban Bargu.”

“Gwamna Badaru ɗan uwa na ne. Tare mu ka fara ACN. Hakan ba ya na nufin ba za mu iya yin takara ba. Ni da shi kamar tagwayen da aka haifa manne da juna ne. Ba mai iya raba mu sai ƙwararren likita.”

Kalaman Badaru Kan Tinubu Sun Yi Karo Da Furucin Sa Kan Amaechi:

2023: Ba Zan Iya Takara Da Amaechi Ba, Saboda Ni Da Shi ‘Uban Mu’ Ɗaya -Gwamna Badaru:

Gwamna Muhammad Badaru na Jigawa ya bayyana cewa ba zai iya tsayawa takarar shugaban ƙasa shi da Rotimi Amaechi a ƙarƙashin APC ba.

Da ya ke jawabi gaban wakilan zaɓen ‘yan takarar shugaban ƙasa a Dutse, a gaban Amaechi, Badaru ya ce a shirye ya ke ya janye wa Ministan Sufurin Najeriya takara, shi Badaru ɗin ya haƙura.

“Wasun ku na san sun fara tunanin cewa Badaru ma ɗan takarar shugaban ƙasa ne. To amma ina tabbatar maku cewa ba za a yi takara tsakani na da Amaechi ba, saboda ni da shi uban mu ɗaya (Shugaba Muhammadu Buhari). Kuma duk mu na girmama uban na mu. Na tabbata kuma za mu tafi ne a kan turba da alƙibla ɗaya.

“Ni da shi duk yaran Shugaba Muhammadu Buhari ne, kuma ya na son mu ƙwarai da gaske. Don haka duk abin da za mu yi, sai da neman tubarrakin sa.

“Don haka ku wakilan zaɓen ‘yan takarar shugaban ƙasa na APC na Jigawa, idan ku ka tuna da ni, to kuma ku tuna da Amaechi, saboda ni da shi duk ‘ya’yan Buhari ne.

“Saboda haka a ranar zaɓen fidda-gwani, ko dai na fito takara, ko kuma shi ya fito. Amma dai tabbas ba zan iya yin takara da shi ba, gara na janye masa.”

Tun da farko tsohon Minista Amaechi ya roƙi wakilan zaɓen ‘yan takarar APC na Jigawa su zaɓe shi, saboda ya cancanta. Ya ce ya fi sauran ‘yan takara sanin Najeriya.

Ya ce idan za a kalle shi, to a dube shi da abin da ya yi a baya, ba abin da ake yaɗawa a matsayin ji-ta-ji-ta a kan sa ba.

Tags: AbujaAhmed LawanAPCBadaruHausaLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Ƴan sanda sun kashe masu garkuwa da mutane uku a Adamawa

Next Post

A BARI YA HUCE KE KAWO RABON WANI: APC ta ɗage ranar tantance ‘yan takarar shugaban kasa

Next Post
IYA RUWA FIDDA KAI: APC ta ce ba za a yi maslaha ba a zaben fidda dan takarar shugaban kasa

A BARI YA HUCE KE KAWO RABON WANI: APC ta ɗage ranar tantance 'yan takarar shugaban kasa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki
  • ƘORAFE-ƘORAFEN MANYAN PDP KAN ATIKU: ‘Zan bi su gida-gida ina sasantawa da su’ – Inji Atiku
  • Sowore ya bayyana Magashi ɗan takarar mataimakin shugaban kasa na AAC, ya ce sai sun yi ragaraga da Kwankwaso a Kano
  • KABILAR MASSAI: Garin Da Ake Tofawa Mutum Majina Da Yawu A Matsayin Sanya Albarka
  • JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.