Zaratan EFCC sun cumuimuyi tsohon Gwamnan Zamfara Abdul’aziz Yari, ta yi awon gaba da shi, bayan an gano ya na da hannu wajen tara Akanta Janar Ahmed Idris kantara satar naira biliyan 80.
EFCC ta shaida wa PREMIUM TIMES cewa ta kama Yari a gidan sa da ke Abuja, bayan bincike ya nuna cewa ya jidi naira kusan biliyan 20 daga cikin naira biliyan 80 ɗin da EFCC ke nema wajen Akanta Janar.
EFCC dai ta kama Ahmed Idris ne cikin makon shekaranjiya, bisa zargin karkatar da naira biliyan 80 da aka ba shi amanar ajiyewa cikin kuɗaɗen Najeriya.
An damƙi Yari a ranar Lahadi a Abuja, kwanaki kaɗan bayan ya ci zaɓen fidda-gwanin Sanatan APC na Zamfara ta Yamma ba hamayya.
An dai yi cacikui da Ahmed Idris tun a ranar 16 Ga Mayu.
A cikin 2021 EFCC ta sha kama Yari bisa binciken yadda ya karkatar da biliyoyin kuɗaɗe, wato wasu daban ba waɗannan biliyan 20 da ake magana a yanzu ba.
Ya yi Gwamnan Jihar Zamfara daga 2007 zuwa 2019.
Discussion about this post