• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

    Masu maular ‘kudaden kama haya’ a hannun Ayu ke hana sasanta rikicin PDP -Wike

    Ministan Abuja ya bada wa’adin gina filaye 189 cikin wata uku, ko ya ƙwace su

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

    Masu maular ‘kudaden kama haya’ a hannun Ayu ke hana sasanta rikicin PDP -Wike

    Ministan Abuja ya bada wa’adin gina filaye 189 cikin wata uku, ko ya ƙwace su

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    DA ƊUMI-ƊUMI: Gobara ta tashi a Kotun Ƙoli, ta babbake ofishin manyan alƙalai uku

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Kotu ta daure magidancin da ya guntile hannun abokinsa kan zargin lalata da matarsa

    Jami’an Kwastam sun kama haramtattun kaya na miliyoyin naira a Katsina

    Hukumar Kwastam ta kama haramtattun kaya na naira biliyan 6.6 a jihar Ogun

    American University of Nigeria Student -Crt- Google

    Malaman jami’o’i na roƙon a biya su albashin wata da watannin da aka riƙe masu

    ‘Yan sanda sun damke faston da ake zargin yayi wa ‘yar shekara 19 fyade

    Kotu ta yanke wa mahaifin da ya yi shekara 9 yana lalata da ƴa’ƴan sa mata biyu

    TSUMAGIYAR KAN HANYA: An umarci ‘yan sandan Abuja su riƙa binciken motar ko wa kuma ko ɗan wa

    Ƴan sanda sun kama magidancin da ya yi wa matar makwabcinsa fyade

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TSADAR ABINCI: Yadda yaƙin Rasha da Ukraniya ya haddasa masifar tsadar abinci a duniya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 9, 2022
in Harkokin Kasuwanci/Noma
0
Muna rokon gwamnati da ta gaggauta samar wa ‘yan Najeriya sauki akan matsanancin tsadar abinci da ake fama dashi a kasa

Kayan abinci da kayan masarufi sun tsawwala tsadar da ƙure aljihun mai ƙaramin ƙarfi, yayin da ‘yan ya-mu-samu ya-mu-sa-bakin-mu ke gaganiyar neman abinci a tsawon rayuwar su ta duniya.

Wannan tsadar rayuwa ta kayan abinci ta yi masifar tashi a cikin watan Maris, sanadiyyar ɓarkewar yaƙin Rasha da Ukraniya.

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) ta ce kayan abinci sun yi tsadar da ba su taɓa yi ba a cikin watan Maris.

Man girki da akamun gwangwani samfurin seralak da nama su ma duk farashin su ya yi sama, kamar yadda ƙididdigar da FAO ta fitar a ranar Juma’a ta nuna.

Rahoton ya bayyana yadda kayan abincin da ba a kai ga dafawa ko sarrafawa ba ya ƙara farashi sosai a faɗin duniya.

Idan aka auna da farashin cikin watan Fabrairu, za a ga cewa a cikin Maris farashin ya ƙaru da kashi 17.9, saurin tashin farashin tun cikin 1990 ba a sake gani ko fuskantar irin sa cikin ƙanƙanin lokaci ba, sai a Maris na watan jiya.

Kayayyaki irin su sugar da madara ta ruwa da ta gari, duk sun ƙara kuɗi, kamar yadda rahoton FAO ya tabbatar.

A Najeriya dai farashin man gyaɗa ya tashi, “haka a duniya duk wani nau’in man girki ya ƙara tsada a cikin Maris.”

“Saboda wasu kayan tilas sai an bi ta tekun ‘Black Sea’ da su, ruwan da a yanzu ya zama lahira kusa, saboda gumirzun yaƙin Rasha da Ukraniya da ake yi a yankin.”

FAO ta ƙara da cewa shi ma farashin man ja da na man waken soya ta yi tashin-gwauron-zabo, saboda neman su da ake yi wurjanjan, dalilin ƙarancin sauran nau’ukan man da safarar su ba ta yiwuwa zuwa wasu ƙasashen duniya, saboda yaƙin Rasha da Ukraniya.

Bayan waɗannan kuma, farashin alkama da nau’ukan su shinkafa da hatsi duk ya tashi a duniya, kuma babban dalilin hakan shi ne yaƙin Rasha da Ukraniya, wanda ya hana jiragen ruwa gangancin giftawa ta ruwan.

“Kasa gudanar da safarar alkama ta cikin ‘Black Sea’ ya haifar da ƙarancin ta da ƙarin farashin ta a duniya.

Alkama na da muhimmanci a duniya, saboda yadda ake sarrafa ta ana samar da abinci kala-kala a duniya.

Farashin alkama a cikin watan Maris ya ƙaru da kashi 19.7 a duniya daidai lokacin da yawancin manoman alkama a Amurka ba su samu albarkar noma sosai a kakar da ta gabata ba.

Kayan gona irin su masara, gero da dawa sun yi ƙarin kashi 20.4 a cikin Maris, masifar tsadar da tun 1990 ba su taɓa yin irin ta ba.”

“Masara ta ƙara tsada da kashi 19.1, saboda Ukraniya ta daina fitar da masara a ƙasashen duniya. Kasancewar Ukraniya ƙasa da ke cikin sahun gaban ƙasashen da suka fi noman masara a duniya, yaƙi ya sa sun dakatar da sayar da masara a waje. Hakan ya sa ta ƙara tsada a duniya.”

“Yayin da Turai naman alade ya ƙara tsada, a saurwn manyan ƙasashen kuma naman kaji ne ya tsula masifar tsada, saboda dakatar da safarar sa daga wasu ƙasashe, saboda ɓullar cutar murar tsuntsaye. Sannan kuma an kasa samun naman kaji daga Ukraniya.

Ba a nan lamarin ya tsaya ba. Tsadar ta shafi naman shanu, ta yadda ƙasashen da ke dogara da sai an shigar masu da naman shanu daga waje, a cikin Maris zuwa yanzu su ke sayen sa da masifar tsada.

Idan mu ka dawo Najeriya, FAO ta ce ‘yan Najeriya kimanin miliyan 19.4 za su fuskanci yunwa da barazanar rashin abinci a cikin Agusta, 2022.

Wannan mumnunan labari ya zo daidai lokacin da ƙasaitaccen attajiri Aliko Ɗangote ya ce “a tashi a yi tanadin kayan abinci, domin yaƙin Rasha da Ukraniya zai haddasa ƙarancin abinci a duniya.”

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya ta tabbatar da cewa aƙalla ‘yan Najeriya miliyan 19.4 ne za su yi fama da yunwa da barazanar rashin abinci tsakanin watannin Yuni zuwa Agusta, 2022.

Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) ta yi wannan bincike tare da haɗin gwiwar Ma’aikatar Harkokin Gona ta Tarayya da wasu Cibiyoyi masu ruwa da tsaki a harkar noma.

Rahoton ya yi nazarin matsalar ƙarancin abincin da za a fuskanta da kuma rashin abinci mai gina jiki a yankunan Sahel da Afrika ta Yamma.

Rahoton ya ƙara da cewa matsalar abinci za ta fuskanci aƙalla jihohi 21 na Najeriya tare da yankin Gundumar FCT Abuja, mai ƙananan hukumomi shida.

An kuma yi kirdadon aƙalla ‘yan gudun hijira 416,000 ne za su tsinci kan su cikin wannan mawuyacin halin tasku.

Sannan kuma rahoton ya nuna a yanzu haka aƙalla mutum miliyan 14.4 da kuma masu gudun hijira 385,000 sun afka cikin wannan halin rigimar gaganiyar ƙarancin abinci, kuma ba za su iya samun kan su a saiti ba, har sai cikin Mayu, 2022.

Jihohin da aka yi nazari a cikin Maris sun haɗa da Abiya, Adamawa, Benuwai, Barno, Cross Riba, Edo, Enugu, Gombe, Kaduna, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi, Legas, Neja, Filato, Sokoto, Taraba, Yobe da Zamfara, dai kuma Gundumar FCT Abuja.

A cikin shekarar da ta gabata dai FAO ta ce aƙalla mutum miliyan 12.8 na ‘yan Najeriya su ka yi fama da fari na ƙarancin ruwan shuka tsakanin Yuni zuwa Agusta, 2021.

Matsalar tsaron da ta dabaibayi samuwar abinci sun haɗa da yaƙin Boko Haram a Barno, Adamawa da Yobe, sai kuma hare-haren ‘yan bindiga a yankin Arewa maso Yamma, a jihohin Sokoto, Katsina, Zamfara, Kaduna da Kebbi. Sai kuma wasu jihohin Arewa ta Tsakiya da suka haɗa da Neja da Benuwai, waɗanda rahoton ya ce su ne lamarin zai fi yi wa riƙon laya a hannun ɗan dambe.

Sannan kuma rahoton ya ce matsalar tsadar kayan abinci da ya haddasa ƙuncin rayuwa a yanzu, zai ƙara ruruta wutar ƙarancin abincin sosai.

Sauran Matsalolin Da Ke Kara Ruruta Ƙuncin Rayuwa Da Rashin Abinci:

“Rashin aikin yi da suɓucewar aikin da mutum ke yi da kuma taguwar kuɗaɗen da magidanci ke samu sakamakon ɓarkewar korona, sai kuma fatattakar da ‘yan bindiga ke wa mutanen ƙauyuka da garuruwa su na yin hijira su zai ƙara kuma ya na ƙara munin matsalolin sosai.”

“Sauran dalilan da su ka sa matsalar ta 2022 za ta zarce ta 2021, shi ne saboda rashin hanyar isa wurin wasu masu gudun hijira da ke cikin lungunan Barno da Yobe, ƙarin munin hare-haren ‘yan bindiga da kuma ƙarin jihohi biyar da aka samu a cikin 2022.” Inji rahoton.

Wakilin Hukumar Abinci ta Majalisar Ɗinkin Duniya (FAO) a Najeriya, Fred Kateero, ya yi kira ga Gwamnatin Najeriya su yi amfani da sakamakon rahoton nan su shata wani tsari na ƙasa bai ɗaya, wanda zai bijiro da hanyoyin zabura a ceto harkar noma nan ba da daɗewa ba.

Ya kuma yi kira ga Gwamnatin Tarayya ta zuba kuɗi sosai wajen tabbatar da samun nasarar wannan shiri.

Tags: AbujaHausaLabaraiNewsPREMIUM TIMESUkraine
Previous Post

Najeriya ce ƙasa ta uku a jerin kasashen da aka fi cin naman kare a duniya

Next Post

ZARGIN YIN HAJIJIYA DA KUƊAƊEN MANIYYATA: Hukumar Alhazai ta gayyaci EFCC domin bankaɗo badaƙala a Asusun Adashen Tara Kuɗaɗen Maniyyata

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Hajji

ZARGIN YIN HAJIJIYA DA KUƊAƊEN MANIYYATA: Hukumar Alhazai ta gayyaci EFCC domin bankaɗo badaƙala a Asusun Adashen Tara Kuɗaɗen Maniyyata

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Mutum sama da 7000 sun kamu da cutar diphtheria, cutar ta yi ajalin mutum 453
  • Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60
  • Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara
  • Yadda Nijeriya Ta Ɗau Saiti Gadan-gadan a Cikin Gida da Waje Ƙarƙashin Mulkin Tinubu, Daga Mohammed Idris
  • Nan da watanni uku, Jami’ar Franco-British za ta fara aiki gadan-gadan a Kaduna – Farfesa Gwarzo

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.