• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

    Nigerian Pilgrims

    HAJJIN BANA: Duk wanda ya zarce shekaru 65 bashi ba Hajji bana – Hukumar Alhazai

    Beggars

    Almajirai da mabarata sun kwararo Abuja – Mahukunta

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    HARƘALLAR KWANGILA: EFCC ta kama Patricia Etteh, tsohuwar Kakakin Majalisar Tarayya

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    Ƴan bindiga sun ƙona hedikwatar karamar hukumar Idemili ta Arewa a jihar Anambra

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    UMARNIN SALLAMA DA KUJERAR MINISTA: Pauline Tallen, Timiprr Sylva duk sun janye daga takara

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Yadda EFCC ta damke Akanta Janar din Najeriya bisa zargin harkallar naira biliyan 80

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Na koma PDP ne don in kawo karshen mulkin kama karyar da APC ke yi a Jigawa – Saminu Turaki

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

    Gumi yayi kakkausar jan kunne ga waɗanda suka kashe Deborah, ya ce ba hurumin su bane yanke hukuncin kisa don an zagi Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Hotunan Da Gwamnatin Nassarawa Ta Yi Amfani da Su Wajen Nuna Aikin da Ake Yi Na Hanyoyin Jihar Na Kasar Brazil ne – Binciken DUBAWA

Silas JonathanbySilas Jonathan
April 7, 2022
in Rahotanni
0
Gwamnatin jihar Nasarawa na kashe naira miliyan 240 duk wata don inganta kiwon lafiya

Abdullahi-Sule Nasarawa

Zargi: A shafinta na Facebook, gwamnatin jihar Nassarawa ta wallafa wadansu hotuna biynu da ta ke zargin titin Sisinbaki-Kwarra ne, wanda ke karamar hukumar Wamba. A cewarta, hotunan na nuna yanayin titin kafin a gyara, da yadda ya zama bayan da aka gyara.

Wajen bayyana daya daga cikin titunan da gwamnatin jihar Nasarawa ta gina a daya daga cikin kananan hukumomin jihar, masu kula da shafin Facebook din jihar sun yi amfani da hotunan Brazil a maimakon hotunan ainihin titin da gwamnatin ta gyara

Hotunan Brazil ne aka sanya a shafin facebook din jihar Nasarawa wajen kwatanta gyaran da aka yi a titin Sisinbaki-Kwarra da ke karamar hukumar Waje.

Sannu a hankali soshiyal mediya ya zama wani bangare na rayuwar yau da kullun. Yayin da ake cigaba da tabka mahawar dangane da sahihancin bayanan da ke cika dandalin sadarwar. Kungiyoyi da wadansu fannonin al’ummar na amfani da shi wajen fadada ayyukansu da manufofinsu.

A dalilin haka ne shafin gwamnatin jihar Nassarwa ta wallafa hotunan gyaran titin da ta ke yi a Sisinbaki-Kwarra, karamar hukumar Wamba a jihar Nasarawan Najeriya.

Shafin na da ma’abota 13,000 kuma yana dauke da dubban hotunan da ke nuna irin nasarorin da gwamna jihar, Injiniya Abdullahi Sule ya yi.

A shekarar 2019 aka zabi gwamnan kuma dan kasuwan a karkashin tutar jam’iyyar APC. Shafin na Facebook na bayyana nasarorin shi tun bayan da ya hau ragamar mulkin jihar.

Irin tsokacin da ke kan shafin na nuna cewa yawancin mutane sun dogara da shafin ne wajen samun bayanan gaskiya dangane da abubuwan da ke faruwa a jihar. Misali, wani mai amfani da shafin ya rubuta wadannan kalaman da ke yabon shafin: “Yana kawo wa jama’a labaran duka abubuwan da gwamnatin ke yi ba tare da an tace wani abu ba, labaran zalla ake kawo wa.”

To amma a zahiri, yaya gaskiyar labaran da ke kan wannan shafin?

Takaddama

Labarin wanda ya nuna hotunan titin kafin a fara aiki da bayan da aka kammala ya ja hankalin jama’a domin mutane sama da 200 sun yi ma’amala da labarin, an raba sau 70. Bugu da kari an sake wallafa hotunan a wasu shafukan na daban irin su tiwita, tare da labarin da aka sanya a shafin Facebook.

Misali, wani mai amfani da shafin Tiwita, mai suna Akashe Abdullahi Ari (@AkasheAri) ya wallafa hoton titin da taken: “Kafin ginawa da bayan gina titin Sissinbaki-Kwarra a Wamba mai tsawon kilometa 15.5. Mun gode gwamna Engr. Abdullahi A Sule.”

To sai dai ba kowa ne a shafin ya gamsu da labarin ba, da yawa sun kalubalanci sahihancin hotunan. Wani mai suna Ibrahim ya nuna rashin gamsuwarsa a yayin da ita ma Joan ta ce “Wannan hoton ba Jihar Nasarawa ba ne. wannan ba gaskiya ba ne.”

Jihar Nasarawa jiha ce a yankin arewa maso tsakiyar Najeriya kuma tana da iyaka da jihohin Filato da Taraba daga gabas, Kaduna daga arewa, jihohin Kogi da Benue daga Kudu dai kuma Birnin Tarayya Abuja daga yammaci.

Tantance Sahihancin Hoton da ya nuna titin lokacin da aka fara gyarawa

Don tantance hoton da ake zargi wai shi ne hoton titin kafin a gyara, mun yi amfani da manhajan Yandex domin gano mafarin hoton.

Manhajar ta Yandex ta nuna mana cewa an fara amfani da hoton ne a wani rahoton da aka wallafa a 2015 wanda ya bayar da cikakken bayani dangane da titin Camacari wanda ke Lauro de Freitas a kasar Brazil.

Hasali ma jaridar Grand Bahia, daya daga cikin manyan jaridun Brazil ce ta yi rahotanni daban-daban dangane da ginin titin. Bacin haka, labarin ya nuna Mateus Pereira na jaridar Grand Bahia a matsayin wanda ya dauki hoton.

Don haka, hoton da ake zargi wai titin Sisinbaki-Kwarra a karamar hukumar Wamba a jihar Nasarawa ne kafin a fara gyarawa ba gaskiya ba ne.

Tantance sahihancin hoton da ke zargin titin Sisinbaki-Kwarra ne bayan an kammala gyara

Da aga yi amfani da manhajan da ke gano ainihin tushen hotuna, sakamakon da aka samu daga kafofin yada labarai da dama sun nuna cewa lallai titin na Sisinbaki-Kwarra ne a karamar hukumar Wamba da ke jihar Nasarawa.

A wani labarin da aka wallafa a Eggonnews, an yi bayanin yadda gwamban jihar ya kaddamar da titin ranar 22 ga watan Mayun 2021.

Wani rahoton da ya bulla a Afridailynewa shi ma ya yi labarin yadda gwamnan ya kaddamar da titin ranar 22 ga watan Mayun 2021.

Rahotannin wadannan jaridun biyu sun yi amfani da wannan hoton. Bacin haka, daya daga cikin hotunan wanda aka yi amfani da shi a Afridailynews ya nuna gwamnan jihar a kusa da wata alama da ta nuna shirin gudanar da aiki a titin Sisinbaki/Kwarra.

To sai dai duk wadannan bayanan ba su gamasar da DUBAWA ba, shi ya sa ta tura wakili zuwa wurin tunda an ce gani ya kori ji. Binciken da aka yi ya nuna cewa hoton da ya nuna aikin da aka kammala a kan titin gaskiya ne. Mazauna al’ummar wadanda suka ga hotunan da aka yi amfani da su a matsayin yadda titin ya ke kafin a fara aiki sun ce ko daya hoton bai yi kama da muhallinsu ba amma wanda aka gama lallai garin su har ma suka kai wakilin DUBAWA wurin ya shaida da kansa.

John Joel wanda ya zagaya da wakilin DUBAWA shi ma ya ce lallai akwai yaudara a hoton.

“Lallai hoton farko ko kusa bai yi da Sisinbaki/Kwarra ba. Ina nan sadda aka fara aikin kuma ba zan iya tuna wani wuri mai kama da nan ba. Amma wanda ke nuna aikin da aka gama nan ne kuma ma zan iya kai ku wurin da kai na.”

Haka nan kuma wani mai mashin Abdullahi Muhammed ya kai wakilin DUBAWA wurin. Daga nan ne DUBAWA ta tabbatar cewa lallai an gina titin Sisinbaki/Kwarra har ma gwamnan jihar ya kaddamar da a shekarar da ta gabata wato 2021. Sai dai hoton da suka yi amfani da shi wajen nuna yadda titin ya ke kafin gyaran ba shi ne ba.

Duk yunkurin da muka yi na ganawa da wadanda ke kula da shafin Facebook na jihar Nasarawar dan jin ta bakin su ya ci tura. Babu wanda ya amsa sakonnin da muka tura a kan shafin na Facebook da ma adireshin email.

Haka nan kuma mun yi kokarin samun jami’an yada labaran gwamnan biyu ta wayar tarho. Shi ma wannan yunkurin ya ci tura domin babu wanda ya amsa wayar har zuwa lokacin da muka yi wannan labarin.

A Karshe

Yayin da DUBAWA ta gano cewa hoton farko ba titin Sisinka/Kwarra da ke karamar hukumar Wamba a jihar Nasarawa ba ne, hoton da aka sa daga baya wanda ke nuna yadda titin ya ke bayan da aka kammala aikin gaskiya ne. Sai dai saboda kasancewar hoton farkon wanda ke da tushe na daban ya sanya alamar tambaya kan sahihancin labarin

Tags: HausaHotunaLabaraiNasarawaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Ɗan shugaban cocin RCCG ya nemi afuwar fastocin cocin da ya kira awakai

Next Post

Shin gaskiya ne mutum daya na iya kasancewa da kwayoyin halitta iri biyu? Binciken DUBAWA

Next Post
KANJAMAU: Akalla mata masu ciki 124,817 ke dauke da cutar a Kanjamau jihar Ondo

Shin gaskiya ne mutum daya na iya kasancewa da kwayoyin halitta iri biyu? Binciken DUBAWA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Walikan Filato na Amaechi ne, babu haufi, babu tantama babu kila wa kala – In ji Lalong
  • MATSALAR TSARO: Nan da wata biyu za a ƙara ɗaukar kuratan ‘yan sanda 10,000 -Dingyaɗi
  • Duk da an ƙara wa Magu girma, za a hukunta shi idan bincike ya tabbatar da laifi a kan sa -Dingyaɗi
  • FASHEWAR TUKUNYAR GAS A KANO: Ministar Jinƙai na so a ɗau matakan hana aukuwar bala’o’i
  • Dalilin da ya sa Buhari ya dakatar da Akanta Janar ɗin da ake zargi da kantara satar naira biliyan 80

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.