Ɗaya daga cikin matan da ke hannun masu garkuwa da fasinjojin da aka kama a harin jirgin ƙasan Abuja zuwa Kaduna, ta haifi jinjira a sansanin ‘yan bindiga.
An dai yi garkuwa da su tun a ranar 28 Ga Maris, 2022, bayan an buɗe wa jirgin ƙasan wuta, ya tsaya.
Sun shafe wata ɗaya cur a hannun masu garkuwa da su, duk kuwa da kiraye-kirayen da jama’a ke yi cewa gwamnati ta ɗauki ƙwaƙƙwaran matakin ceto su.
Kwanan bayan ‘yan ta’addar sun saki bidiyo biyu, inda su ka nuno waɗanda ke tsare a hannun su, har su na jawabin a gaggauta ceto su ta hanyar sasantawa da waɗanda ke tsare da su.
Bidiyon ya ɗan kwantar da hanulan iyalan waɗanda ke tsare, inda su ka samu tabbacin ba a kashe waɗanda aka tsare ɗin ba.
To amma kuma murna ta koma ciki, ganin yadda ‘yan ta’addar su ka gindiya wa gwamnatin tarayya tsauraran sharuɗɗan da sai an cika masu sannan za su sake su.
Duk da dai ba a fito an ce ga sharuɗɗan ba, amma rahotanni sun nuna cewa su na so ne a saki wasu gaggan ‘yan ta’adda ne su 16 da ke tsare.
Makonni biyu da su ka gabata, Ministan Yaɗa Labarai Lai Mohammed ya ce gwamnatin tarayya na ƙoƙarin ganin ta ceto waɗanda ke tsare ɗin. Sai dai kuma har yau shiru ka ke ji, domin ga shi har mai tsohon ciki daga cikin waɗanda ke tsare ɗin ta haihu a hannun su.
Rahotanni sun tabbatar da haihuwar mai tsohon cikin, wadda ɗaya ce daga cikin mata biyu masu cikin da ke hannun ‘yan ta’addar.
Majiya ta ce ‘yan ta’addar sun kai wa matar likitoci da nas-nas da kayan da mai haihuwa ke buƙata a cikin daji, domin tabbatar da cewa ta haihu lafiya.
Tun cikin makon jiya ta haihu, aka sai a ranar Laraba dangin ta suka samu labari, yayin da ‘yan ta’addar su ka aika masu da sanarwar haihuwar ta.
Dangin matar sun ce an kai mata likitoci da nas-nas da kayan agajin mai haihuwa, inda ta haihu a bisa kulawar likitoci.
Sun ce ‘yan ta’addar na neman a sako wasu kwamandojin su kafin su saki wadanda ke a hannun su.
“A cikin makon nan suka sanar da mu haihuwar ta. Amma ba a ce mana mace ta haifa ko namiji ba.” Haka majiya daga cikin dangin ta ta tabbatar.
Mu Na Ƙoƙarin Ceto Matafiyan Jirgin Ƙasa Da Ke Hannun ‘Yan Ta’adda -Gwamnatin Tarayya:
Ministan Yaɗa Labarai, Lai Mohammed ya ce ba za mu shaida wa ‘yan jarida ƙoƙarin da gwamnati ke yi don ceto waɗanda aka kama ba.
Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ta na yin dukkan ƙoƙarin da ya dace wajen ganin ta ceto dandazon fasinjojin jiragen da aka yi garkuwa da su a dajin Kaduna, ciki watan Maris.
Ministan Yaɗa Labarai Lai Mohammed ne ya bayyana wa manema labarai haka a Faɗar Shugaban Ƙasa, jim kaɗan bayan kammala taron Majalisar Zartaswa ta Ƙasa, a ranar Laraba.
Mohammed ya ce duk da dai ba zai bayyana wa ‘yan jarida takamaiman irin ƙoƙarin da ake yi ba, “amma dai ina tabbatar ma ku da cewa a yanzu ɗin nan da mu ke magana, ɓangaren gwamnati daban-daban na can na yin ƙoƙarin ganin an ceto mutanen da ran su da lafiyar su.”
Minista Lai Mohammed ya ƙara da cewa “abin da gwamnatin tarayya ke yi ba abu ba ne da za a fito a wurin taron manema labarai ana yayata shi ba.
Ya ce musamman saboda akwai butun rayuwar waɗanda ake tsare da su, kada lamarin ya dagule masu.
“Amma dai ɓangarorin jami’a tsaro da dama na aiki ba dare, ba rana domin bin-diddigin yadda harin da garkuwar su ka faru domin lalubo yadda za a ceto su da ran su da lafiyar su.”
PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda aka kai wa jirgin hari a ranar 28 Ga Maris, bayan jirgin ya bar Abuja, kan hanyar sa ta zuwa Kaduna, tsakanin Katari.
Aƙalla mutum 8 aka bada rahoton mutuwar su.