A wani Binciken Haɗin Guiwa Tsakanin American University of Nigeria (AUN) da PREMIUM TIMES wanda Jacob Udo-Udo Jacob ya yi binciken a madadin ɓangarorin biyu ya nuna yadda ambaliyar cima-zaune da dandazon matasa zai zame wa Najeriya matsala nan da shekaru 10.
Wannan rahoton kashi na farko ne daga cikin kashi biyar ɗin da ke tafe nan gaba daki-daki.
Nan da shekaru 10 zuwa sama, Najeriya za ta fuskanci gagarimar matsalar miliyoyin cima-zaune, waɗanda ba su iya ciyar da kan su, sai dai a ciyar da su.
*Bincike ya nuna nan da shekara 10 kashi 43 cikin 100 na ‘yan Najeriya, za su kasance duk cima-zaune ne, wato daga jinjirai zuwa ‘yan shekaru 14 da haihuwa.
*Yawan waɗannan cima-zaune zai kasance mafi yawa a Najeriya, idan aka kwatanta da na sauran ƙasashen duniya.
*Nan da shekaru 10 kenan yawan cima-zaune a Najeriya da dandazon matasan da ba su da takamaimen alƙibla a Najeriya zai kai kashi 25 bisa 100 a duniya baki ɗaya.
*Matsalolin da za su dabaibaye Najeriya nan da shekaru 10, sun haɗa da yawan ƙananan yara barkatai da yara cima-zaune da kuma matasa marasa kishin tashi su yi ilmi, ko waɗanda ba su samu damar yin ilmin ba.
Wannan matsala za ta haifar da barazana ga abinci, barazana ga tsaro da kuma kwararar masu gudun hijira.
1 – Idan aka duba ƙasashe masu maƙautaka da Najeriya irin su Nijar, Mali da Chad, za a ga nan da shekaru 10 yawan cima-zaunen su zai kai Mali kashi 50 bisa 100, Nijar kashi 47 bisa 100 sai Chadi kashi 46 bisa 100 na yawan al’ummar kowace a cikin ƙasashen uku.
2 – Ƙarancin abinci da rashin aikin yi ga matasa zai haifar da kwararar ‘yan gudun hijira daga waɗancan ƙasashe zuwa cikin Najeriya.
3 – Akasarin waɗanda za su kwararo Najeriya za su ƙara wa ƙasar nauyin matsaloli ne, domin a cikin su babu wasu ƙwararru ko masu ilmin da ƙasa za ta amfana da su ne (kamar likitoci ko malaman makaranta ko masu fasaha), duk masu neman abincin sa wa bakin salati ne.
4 – Akwai kuma fantsamar matasa masu tsatstsauran addini nan gaba, waɗanda matsalolin da ƙasashen su ke ciki za su iya kwarara Najeriya. Waɗanda ba sana’ar neman abinci su ka iya ba, za su fake ko jingina da malaman da za su kasance su ne idon su su ne alƙiblar su a duniya. Tsatsauran ra’ayin da za su ɗauka a matsayin mafita daga ƙuncin rayuwa, wanda su ke ganin shi ne hanyar tsira gobe kiyama, zai zame masu da da kuma al’umma matsala.
5 – Akwai yiwuwar ta’addancin da hare-haren ‘yan bindigar da ake fama a cikin dazuka ya fantsama har cikin garuruwa, a kasa zaune, a kasa tsaye.
Ƙasa samun ilmin zamani ga ɗimbin matasa da kuma fatara da yunwa zai ƙara haifar da kwarara zuwa cikin birane da kuma kwararar baƙin-haure zuwa zuwa cikin Najeriya. Tunda matasa ne yawanci, za su zame wa al’umma alaƙaiƙai.
6 – Wasu ƙungiyoyin addini masu tsatsauran ra’ayi za su bayyana. Kamar yadda bayan bayyanar Maitatsine cikin shekarun tamanoni (1980s) ya buɗe ƙofar bayyanar wasu ƙungiyoyi bayan shekaru da dama, irin su Boko Haram da ISWAP.
7 – Ko da a yanzu an ga bayan ƙungiyoyin ta’addanci da na ‘yan bindiga, to aƙidar ta’addancin ba za a iya kankare ta a zukatan matasa ba.
8 – Akwai gagarimar matsalar canjin yanayi wanda zai haifar da ƙarancin abinci, rashin tsaro za su haddasa kwarara cikin garuruwan ƙasar nan.
9 – Hasashen ya nuna yadda za a samu yawaitar ɗimbin masu amfani da wayar hannu da kuma damar shiga intanet, wadda za a riƙa yawan aiki da ita ta hanya mai kyau, ko akasin haka.
10 – Mafita daga wannan matsala shi ne a fantsama wajen zuba jarin gina ƙasa da kuma gina al’umma. Sannan a bijiro da gagarimin aikin bunƙasa ilmin zamani ga yara ƙanana da kuma matasa.
Discussion about this post