• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    ZAƁEN KANO: Ganduje, Gawuna Garo da APC sun ƙi amincewa da sakamakon zaɓe, sun yi zanga-zanga a Kano

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Ba ayi zabe a Katsina ba, coge aka yi kuma za mu garzaya Kotu – Lado-Danmarke

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Hyacinth Alia na APC ya lashe zaben gwamnan jihar Benuwai

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    Umar Bago na APC ya lashe zaben gwamnan Neja

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    KURUNKUS: Abba Gida-Gida ya doke ɗan takaran Uban Abba, Gawuna na APC da kuri’u sama da miliyan ɗaya a Zaɓen gwamnan Kano

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    ZAƁEN GWAMNAN JIGAWA: Namadin APC ya natsar da Lamidon PDP a Jigawa, ya lallasa shi da kuri’u 618,449

    Thugs-attack-collation

    ZAƁEN GWAMNONI YA ƊAU ZAFI: An kashe shugaban PDP bayan an lakaɗa masa dukan tsiya a rumfar zaɓen sa

    2023: Ya mutan Adamawa, ga Tinubu ga Binani na kawo muku su – Shelar Buhari a Yola

    ADAMAWA TA KWASHI ‘YAN KALLO: Binani ta kamo hanyar tururmusa ƙarti 14 a kokawar ƙwace kujerar gwamna

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

    INEC ta dage zabe a rumfuna 10 a jihar Legas

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Dalilai 9 da su ka sa Buhari bai saka hannu a kwangilar samar da na’urorin hangen bam da ‘yan bindiga daga nesa ba

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
April 2, 2022
in Manyan Labarai
0
Dalilai 9 da su ka sa Buhari bai saka hannu a kwangilar samar da na’urorin hangen bam da ‘yan bindiga daga nesa ba

Rashin bayar da gamsasshen bayani da hujjojin yadda za a sayo na’urorin da kuma tabbacin kamfanin da zai yi kwangilar, sun haddasa samar da jinkiri da kuma ƙin amincewar Majalisar Zartaswa a kwangilar sayen na’urorin hangen bam da ‘yan bindiga daga nesa, wadda Ministan Sufuri Rotimi Amaechi ya gabatar wa Majalisar Zartaswa kimanin watanni shida kafin ‘yan bindiga su kai mummunan farmaki kan jirgin ƙasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a ranar Litinin.

Wata takarda ko wasiƙar sirri da ta faɗo hannun wannan jarida ta nuna yadda Majalisar Zartaswa ta yi fatali da wata kwangila da Amaechi ya nemi bayarwa a ƙudundune.

Amaechi ya nemi Majalisar Zartaswa ta amince da kwangilar sayo na’urorin hange da tantance bam ko ‘yan bindiga daga nesa da aka yi niyya maƙala wa jiragen ƙasa daga Abuja zuwa Kaduna.

Majalisar Zartaswa ta ƙi amincewa ne saboda waɗansu dalilai da suka haɗa da:

Na farko dai Minista Amaechi ya kasa bayar da hujjar cewa kamfanin da zai bai wa kwangilar zai iya kawo kayayyakin.

Sannan Amaechi bai gamsar da Majalisar Zartaswa cewa kamfanin zai iya aikin maƙala na’urorin idan ya shigo da su ƙasar nan ba.

Dalili na uku, Majalisar Zartaswa ba ta amince da kwangilar ba, saboda aiki ne na maƙudan kuɗaɗe, har naira biliyan 3 da ɗoriya. Amma kamfanin da Amaechi ya yi niyyar bai wa kwangilar kwata-kwata bai taɓa yin irin wannan aikin ba.

Wani dalili kuma shi ne Minista Amaechi ya kasa gabatar wa Majalisar Zartaswa irin wasu ayyukan da kamfanin ya taɓa yi a baya, ballantana a gamsu cewa zai iya yin aikin samar da na’urorin.

Sannan kuma Amaechi bai kawo hujja daga wani wuri mai nuna cewa akwai inda aka yi amfani da irin na’urorin kuma a yanzu haka su na aiki sosai.

Wani dalili kuma shi ne, Majalisar Zartaswa ta gano cewa kamfanin da Amaechi ya bai wa kwangilar ɗan tagajan-tagajan ne, gaba ɗaya abin da ke cikin asusun kamfanin bai wuce naira miliyan 84.9 ba.

Sannan kuma kamfanin bai wuce shekaru uku da kafawa ba. Domin an kafa shi ne cikin 2019, sannan kuma ba shi da wata ƙwarewa ko gogewar yin irin ayyukan da Amaechi ya nemi a ba shi.

Wani dalilin kuma shi ne, Amaechi bai gabatar Da sunayen wasu kamfanonin da su ka nema aka hana su ba, ballantana a auna ta su ƙwarewar ko cancantar da kuma ta ɗan tagajan-tagajan ɗin kamfanin da Amaechi ya nemi bai wa kwangilar ba.

Wani dalilin kuma shi ne Amaechi bai yi wa kwangilar dalla-dalla ba. Kamata ya nuna cewa za a kashe kuɗaɗen a jirgin ƙasa masu zuwa garuruwa kaza da kaza. Shin iyakar masu zirga-zirga Abuja da Kaduna ne, ko kuwa har da na sauran garuruwa za a kashe wa kuɗaɗen? Duk Minista Amaechi bai yi haka ba.

Idan ba a manta ba, bayan kai hari kan jirgin ƙasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna, Amaechi ya bayyana cewa “da tun tuni an maƙala wa jiragen da ke zirga-zirga tsakanin Abuja da Kaduna na’urorin, to da hakan bai faru ba.”

Sai dai kuma Amaechi bai wa duniya cewa shi ne ya haddasa sakacin ba, saboda ya bayar da kwangilar aikin samar da na’urorin a ƙudundune, kuma ga kamfanin da bai cancanta ba.

“An tsaya ana jayayya akan aikin samar da na’urorin na jiragen ‘drone’ kyamara mai-gani-har-hanji’. Ana buƙatar waɗannan na’urori domin ko daga nesa jirgi ya ke, za su nuna masa akwai matsala daidai wuri kaza da kaza. Idan wasu mutane ne ɗauke da makamai, duk na’urorin za su sanar.” Inji Amaechi.

Amma wasiƙar ƙin amincewa da ƙudundunen da Amaechi ya yi, ta faɗo hannun PREMIUM TIMES, wadda a Taron Majalisar Zartaswa na ranar 24 Ga Satumba, 2021, aka ƙi amincewa da kwangilar naira biliyan 3.7 ɗin da Ministan na Sufuri ya nemi bayarwa a sunƙaƙe.

Batutuwan da aka tattauna a wurin taron waɗanda aka rubuta, sun faɗo hannun wannan jarida. Sun nuna wani kamfani ne mai suna Mogjan Nigeria Limited wanda aka yi wa rajista a ranar 6 Ga Agusta, 2019 Amaechi ya so a bai wa Kwangilar.

Majiyar Fadar Shugaban Ƙasa ta shaida wa jaridar Punch cewa an ƙi amincewa da kwangilar saboda, “mun yi tantama da tababar ƙwarewar kamfanin, wanda bai ma fi shekaru biyu da kafuwa ba.

“Sannan kuma kamfanin bai taɓa yin aikin da ya kai naira biliyan 3.7 a baya ba. Bai kuma taɓa samar da na’urorin a wani wuri an tabbatar da ƙwarewar sa ba.”

A cikin wasiƙar dai an rubuta cewa Amaechi ya shaida wa Majalisar Zartaswa cewa Hukumar Tantance Kwangiloli ta Ƙasa (BPE) ce ta amince da kamfanin.

Tsakanin Tashar Jirgin Ƙasa ta Idu da ke Abuja da Tashar Jirgin Ƙasa ta Rigasa a Kaduna, tazarar kilomita 200 ce. A can ne Amaechi ke so a kashe zunzurutun naira biliyan 3.7.

Shi kan sa Mataimakin Shugaban Ƙasa Yemi Osinbajo wanda ya jagoranci Taron Majalisar Zartaswa a ranar, ya umarci Amaechi cewa ya na so ya san yadda na’urorin za su riƙa aiki idan ana amfani da su tukunna.

Shi kuwa Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa Ibrahim Gambari, ya nemi sanin shin a tsakanin jiragen Abuja da Kaduna kaɗai za a kashe kuɗaɗen ko har da na sauran garuruwa?

A nan ne Amaechi ya ce ai aikin na gwaji ne, idan ya yi sosai a tsakanin Abuja zuwa Kaduna, to kuma sai a yi a sauran garuruwan da jiragen ƙasa ke zirga-zirga.

Tags: AMaechiHausaJirgin KasaLabaraiPREMIUM TIMES
Previous Post

Ƴan bindiga sun kashe ƴan kasuwa 7 sun sace wasu da dama a kasuwan Ƴantumaki, Katsina

Next Post

MATSALAR TSARO: ‘Yan sanda sun kama lodin albarusan harbo jiragen sama a tashar mota a Maiduguri

Next Post
MATSALAR TSARO: ‘Yan sanda sun kama lodin albarusan harbo jiragen sama a tashar mota a Maiduguri

MATSALAR TSARO: 'Yan sanda sun kama lodin albarusan harbo jiragen sama a tashar mota a Maiduguri

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 11 da ake so a yawaita yi a watan Ramadan
  • ZABEN KADUNA: PDP ta yi murdiya a wasu kananan hukumomi, zan Kalubalance su a Kotu – Uba Sani
  • SABUWAR ƁARAKA A PDP: An dakatar da Fayose, Anyim, Gwamna Ortom zai gurfana gaban kwamitin ladabtarwa
  • Yunƙurin ‘yan majalisar APC uku masu so a halasta tu’ammali da tabar wiwi ya samu cikas
  • ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Keyamo ya roƙi SSS su kama Obi da Datti, saboda furucin cewa ‘zaɓen 2023 daidai ya ke da mulkin soja’

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.