Gwamnatin Tarayya ta bada umarnin daga ranar Talata, 4 Ga Afrilu a kulle duk wani layin wayar da mai shi bai haɗa da lambar katin shaidar ɗan ƙasa (NIN) ba.
Wata sanarwar da Kakakin Hukumar Sadarwa ta Ƙasa (NCC) shi da Kakakin Hukumar Rajistar Katin Shaidar Ɗan Ƙasa (NICM) su ka sa wa hannu, ta bayyana cewa “duk layin wayar da aka kulle daga ranar Talata, ba za a buɗe shi ba, har sai an yi masa rajistar haɗa shi da lambar NIN ɗin mai shi tukunna.”
Sanarwar mai ɗauke da sa hannun Ikechukwu Adinde na NIN da Kayode Adegoke na NICM da suka fitar a ranar Litinin, ta ce “Shugaba Muhammadu Buhari ya amince daga ranar 4 Ga Afrilu, 2022 a kulle duk wani layin wayar da mai shi bai haɗa shi da lambar katin shaidar ɗan Najeriya ba ta NIN. Sai ranar da ya haɗa sannan za a buɗe masa.
“Kuma an haramta wa layin nasa yin kira, har sai ya yi rajistar haɗa layin da lambar sa ta NIN tukunna.”
An dai bada umarnin kulle layukan ne bayan da aka riƙa ɗage ranar kullewar har sau 10, tun bayan fara yin aikin rajistar haɗa layukan waya da lambar NIN a cikin Disamba, 2020.
Tun farko dai an bijiro da tsarin ne domin a daƙile masu garkuwa da mutane su na neman kuɗin fansa.
Hakan ya sa Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin Ma’aikatar Sadarwa ta Ƙasa ta bijiro da tsarin, a matsayin dabarar gano ɓatagari, da kuma lambar da su ka yi kira da ita.
Sai dai kuma duk da kusan lambobin waya miliyan 125 ne aka nemi a haɗa su da NIN, har yau mutum miliyan 78 ne kaɗai su ke da kati ko lambar shaidar ɗan ƙasa (NIN).
Sannan kuma har yau ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane na ci gaba da amfani da layukan waya masu rajista da marasa rajista su na kiran iyalan waɗanda suka kama, ana kai masu kuɗin fansa.
Discussion about this post