Gwamnan jihar Ribas Nyesome Wike ya ce lallai gwamnan Edo ya shiga taitayin sa domin shi ba sa’an sa bane a jam’iyyar PDP yana mai cewa zai zuke shi kamar hayaki tare da ‘yan koron sa.
Wannan shine martanin da wike ya maida wa gwamna Obaseki bayan kalaman da ya yi akan sa cewa jam’iyyar PDP ba gadon gidan sa bane.
Gwamnan jihar Edo ya maida wa gwamnan Ribas Nyesome Wike martani inda ya gard’gaɗeshi da ya daina yi wa jam’iyyar bababkere ya na yi kamar PDP gadon gidan su ne babu wanda ya isa da jam’iyyar.
Obaseki ya ce mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shuaibu bai yi barazanar ficewa daga jam’iyyar ba kamar yadda Wike ya ce, shi Wiken ne yake yi wa jam’iyyar barazana akai akai.
” In banda nuna isa ace wai mutum shi kadai a kullum sai ya rika nuna babu wanda ya isa da shi a jam’iyyar PDP, kamar gadon gidan su, dole yadda yake so kowa sai dai yabi shi, ba za ta saɓu ba.
” Dukkan mu ƴaƴan jam’iyya ne kuma kowannen mu na da iko akan jam’iyyar kamar kowa. Saboda haka ya daina huhhura hanshi yana yi wa mutane babakere kamar shine kaɗai wanda ya isa akan jam’iyyar.
Obaseki ya zargi Wike da mataimakin Jam’iyyar na yankin kudu Maso Kudu Dan Orbih da yi kutunguilar kawo ruɗani a jihar.
” Ina son Wike da ƴan koron sa su sani cewa ba za su iya kawo ruɗani a cikin PDP ba kamar yadda suka yi a jihar Cross Ribas saboda neman jam’iyyar ta tsaida shi takarar shugabancin Najeriya a 2023.
Kalaman da mataimakin gwamnan jihar Edo babu ruɗani a cikin sa. Yayi magana ne a matsayin shi na matashi domin matasan Najeriya. Idan Wike ba zai iya sauraren korafin matasa ba, yaya zai yi da su a vurin sa na zama shugaban kasa da yake da shi.
Wike ya ce idan ba a hukuntashi ba bisa kalaman da yayi, zai yi amfani da karfin Idon da yake da shi ya hukunta shi da karfin tsiya ko jam’iyya ta so ko bata so ba.
Martanin WIKE
” Da farko dai zan fara da aika sakon neman gafara ne ga tsohon gwamnan jihar Adams Oshiomhole da ya ya rika ja mana kunne cewa Obaseki ba mutumin kirki bane muka yi masa kunnen uwar shegu. Ga shi yanzu ya nuna mana kakara cewa ashe dai da gaske ne butulu ne shi.
” Ni ba sa’an ka bane a PDP kuma ina son ka koma ka gaya wa ‘yan koran ka cewa nafi karfinsu. Zan yi watsawatsa da su. Takarar shugaban kasa ne zan yi kuma ba su isa su hana ni fitowa. Ka koma ka gaya musu su da suka turo ka.
” Ni ne nan Darektan Zaben ka a PDP a lokacin da ka nemi takara a karkashin jam’iyyar. Na yi maka kuma tare da matanka kuka zo nan jihar yi mini godiya. Amma yanzu kana wage baki kamar ba kai ne jiya kake neman mu ruwa ajallo ba.
Wike ya ce dama Obaseki dan haya ne a gidan PDP.
Discussion about this post