A Matsayina na Ɗan Jihar Zamfara kuma mai Haƙƙi Da Dukiyar jihar Zamfara dakuma Gwamnatin jihar Zamfara Nayi Allah waddai Da Kyautar Motoci kirar Hilux Da Gwamnatin jihar Zamfara Tayyi Da Sunan Wai Za’a Cigaba da Yaƙar Ƴan Ta’addah a wasu yankuna.
A Dai-dai Lokacin da Ƴan bindiga suke kai munanan Hare-hare Ta’addanchi A wasu Sassa Daban-daban na Jihar Zamfara A Lokacin Gwamnatin jihar Zamfara Take Bukin Bada Kyautar Motoci kirar Hilux ga ƙasar Niger domin Yakar Ƴan Ta’addah A Yankunan su.
Cikin Mutuntawa da Girmamawa Ina Amfani Da wannan Dama Inyi Kira Ga Mai Girma Gwamnan jihar Zamfara (Dr Bello Muhammad Matawalle maraun) Daya Dubi Yiyuwar Chanza Salon Yaƙin Ƴan Ta’addah da miyagun Ayukka A wannan jihar Ta Zamfara.
Sanin Kowane Al’ummar Jihar Zamfara Har Yanzu Suna Fama Da Munanan Hare-haren Ƴan Bindiga daga kowane Yanki a Faɗin Jihar kazalika mutane suna Cikin Tsoro da Rashin Tabbas Dakuma Samun Halin Ko’oho daga. Gwamnatin jihar Zamfara Musamman a wannan Sha’ani na Tsaro wanda Yaƙici yaƙi cinyewa A Jihar.
Mai Girma Gwamna Nasan Kana Sane Da Munanan Hare-haren ƴan bindiga da suke Faruwa A Cikin waɗannan Makonnin, kuma Nasan Gwamnatin jihar Zamfara tanada labarin Waɗannan Hare-haren wanda Sukayi Sanadin Hasarar Rayukka Dadama A jihar Zamfara.
A Nawa Tunani A Iya Hangena Dakuma Ƙaramin Ilimi da Nike dashi Banga Amfanin Kaiwa wata ƙasa ɗauki A wannan Gaɓar da muke ciki Alhali ga jiharka ta Zamfara tana fama da waɗannan munanan Hare-hare.
Babu Amfanin baiwa ƙasar Nijar Tallafin motocin Yaƙin Ƴan Ta’addah da miyagun Ayukka Alhali Jihar Zamfara muna Fama da Ire-iren waɗannan Miyagun Hare-haren Waɗanda suka Ninka na Niger Da Rinjaye mai nauyi.
Kirana Ga Gwamnatin jihar Zamfara dashi kanshi Mai Girma Gwamnan jihar Zamfara.
Don Allah A dubi Yiyuwar Chanza Salon Ƴaƙin Ƴan Ta’addah A wannan Jihar A Dubi Yiyuwar Canza dubaru waɗanda suke masu Amfani Adubi Yiyuwar Keɓantarda matsalar nan ta tsaro Ayimata karatun Tanatsu A Cire Kowane irin Son zuciya A Yiwa Matsalar Tsaron Jihar Shiri na musamman domin Ganin An ceto waɗannan yankuna dakuma ita kanta jihar daga waɗannan Fitintinu.
Allah Yabamu zaman lafiya mai ɗorawa Ajihar Zamfara da Najeriya Yakuma bamu Yalwatuwar arziki da ɗaukaka Ya Toni Asirin Duk mai Hannun acikin wannan aika-akar.
Hamdan Alhazzai Shinkafi
(JAGABA JR).
Discussion about this post