A cigaba da ganawa da tattaunawa da yake da masu ruwa da tsaki a harkar siyasar jihar Kaduna, kwamishinan kasafin kudin jihar Kaduna Mohammed Abdullahi ya yi tattaki zuwa babban birnin tarayya domin yin ziyara ga ƴan majalisan jihar dake Abuja.
Idan ba a manta ba Dattijo ya bayyana ra’ayin sa na fitowa takarar gwamnan jihar Kaduna a 2023 bayan gwamna mai ci Nasir El-Rufai ya kammala wa’adin sa na mulkin jihar.
A wannan ziyara da ya kai ranar Laraba, Dattijo ya lunƙaya ofishin sanata Uba Sani wanda shima ya kaddamar da nashi takarar don gwamnan jihar Kaduna a garin Kaduna ranar Talata.
Bayan haka ya ziyarci ƴan majalisan jihar dake wakiltan Kaduna a majalisan tarayya.
” Na yi tattaki ne zuwa majalisar kasa domin in gana da babban yayana, sanata Uba Sani da sauran ƴan majalisan jihar dake Abuja domin in sanar musu niyya ta na fitowa takarar gwamnan jihar Kaduna a 2023.
Bayan Sanata Uba Sani, Dattijo ya leƙa ofishin Sanata Abdu Kwari domin mika gaisuwarsa.
Da Dattijo da Sanata Uba Sani duk makusantan gwamna Nasir El-Rufai ne na kud da kud.
A jam’iyyar PDP ita ma a jihar tana da ƴan takara da suka bayyana ra’ayin su na yin takarar gwamna jihar. Kan gaba cikin su shi ne Honarabul Isah Ashiru, Shehu Sani, Datti Baba Ahmed da dai sauran su.
Discussion about this post