Babban ɗan tsohon shugaban kasan Najeriya, Marigayi Sani Abacha, Mohammed Abacha ya yabawa shugaban jami’ar Maryam Abacha dake Nijar da Najeriya saboda raɗa wa jami’ar sunan mahaifiyarsu da yayi.
A hira da yayi da Tubeless, Abacha ya ce wannan karamci da Farfesa Gwarzo yayi abin alfahari ne garesu da ita mahaifiyar ta su.
” Farfesa Gwarzo ƙanine a wajen sanan ɗane a a wajen mahaifiyar mu. Abinda yayi ya yi matukar faranta mana rai da kuma uwar mu. Sannan kuma abinda yake yi abu ne mai kyau matuka musamman a wannan lokaci da ake bukatar faɗada ilimi a musamman yankin Arewacin Najeriya.
” Idan ka duba za ka ga cewa jami’a ce wacce aka fara kafata a ƙasar Nijar, yanzu gashi a hankali jami’ar ta zarce kasar an buɗe sabuwa a Najeriya.
A cikin kwanakinnan ya ke ce min daga kasar Ghana ma an zo musamman domin rokon iri. Suna son farfesa Gwarzo ya buɗe irin wannan jami’a a Ghana. Dole mu gode masa matuka sannan mu ruka bin sa da addua.
A karshe Abacha ya mika sakon godiya ga farfesa Gwarzo yana yi masa fatan alkhairi da kuma jinjina masa kan wannanaiki na ilmantar da mutane da yake yi musamman a wannan yanki namu na Arewa da ilimin zamani yayi ƙaranci a ciki.
Farfesa Gwarzo ya kafa jami’ar Maryam Abacha a kasar Nijar shekaru kusan 7 da suka wuce, sannan yanzu haka ya kafa irin wannan jami’a a Najeriya.
Discussion about this post