Sakamakon binciken da Kungiyar kiwon lafiya ta duniya WHO ta gudanar ya nuna cewa mata akalla kashi 33% ne mazajen su ke cin zarafinsu a duniya.
Binciken ya kara nuna cewa kashi daya bisa uku na mata masu shekara 15 zuwa 49 sun kai karan yadda mazajen su ke cin zarafinsu a duniya.
WHO ta ce mafi yawan lokutta matan da mazajen su ke cin zarafin su basu iya barin auren su duk da cewa mazajen su na cin zarafinsu.
A Najeriya rashin samun ilimin boko, talauci da rashin samun karfin gwiwar kai karar mazajen mata na daga cikin matsalolin dake hana a kwato wa matan dake fama da irin wannan matsala hakkunan su.
Damilola
Wata matar aure kuma mahaifiyar ‘ya’ya uku mai shekara 25 Damilola Lake ta bayyana cewa ta auri mijinta Israel Alake a shekarar 2018.
Damilola ta ce a lokacin da ta auri mijinta tana da shekaru 21 sannan tana koyan yin kwalliya irin na zamani da ake yi wa mata lokacin buki.
Ta ce mijinta Israel aikin wutan lantarki yake yi a lokacin sannan yana yawan yi mata kyautan kaya da kudi. Ta ce kafin su yi aure Israel ya yi mata alkawarin bude mata shago domin ta ci gaba da sana’ar yi wa mutane kwalliya.
Damilola ta ce mijinta ya canja bayan sun yi aure sun haifi ya’ya biyu.
Ta ce a lokacin ya fara wulakanta ta tare da yi mata dukan tsiya, Israel baya kula da ita da ‘ya’yan ta sannan duk alkawarin da ya dauka mata kafin su yi aure ya ki cikawa.
Damilola ta ce wata rana ta fita yin cefane inda bayan da ta dawo ta iske kayanta a waje wasu ma an zubar da su a kwata.
Ta ce tare da rokon makwabta da kyar Israel ya fito ya bayyana laifin da ta aikata cewa wai ta fita ba tare da izinin da ba kuma ta bar ‘ya’ya da yunwa.
Damilola ta ce yanzu haka tana jinyar raunin da Israel ya ji mata a wani dukan da ya yi mata a kwanakin baya.
Ta ce baza ta iya barin auren ta ba duk da wahalan da take Sha saboda naira 10,000 take samu a wata sannan gata da yara uku.
Damilola ta bayyana wa PREMIUM TIMES Damilola ta roki gidan jaridar da kada su fadi sunan ta sannan kada su bari mijinta Israel ya sani saboda idan ya sani zai kashe ta.
Zainab Ilias
Zainab Ilia’s mai shekara 27 ta ce ta auri mijinta Imran Ilias bayan ta rubuta jarabawar JAMB sau shida ba ta yi nasara ba.
Ta ce ta auri Imran a shekaran 2017 sannan a lokacin ya yi alkawarin taimaka mata ta ci gaba ta karatunta na Boko.
Zainab ta ce Imran yana da digirin Amma ta ce tun bayan da ta aure sa ya fara cin zarafin ta.
Ta ce Imran na yi mata gorin rashin shiga jami’a baya ga dukan da yake mata sannan da rashin kula da yake wa ita da ‘ya’yan ta.
Zainab ta ce tayi tsawon shekara uku ba tare da ta ga iyayen ta ba saboda Imran ya hanata.
Ta ce a shirye take ta ci gaba da zaman auren Imran saboda ‘ya’yan ta Kuma saboda Bata da kudin ta za ta iya kula da kanta ta ‘ya’yan ta idan ta fita daga auren ta.
Zainab ta ce idan Imran zai Kara aure ya yi amma ya tabbatar yana kula da iyalinsa.
Matakin da ya kamata a dauka
Kungiyar ‘Spotlight Initiative’ ta hada hannu da European Union (EU), United Nations (UN) da kungiyoyin kare rajin dan Adam domin tsara matakan da za su taimaka wajen kare hakkin matan da mazajen su ke cin zarafinsu.
Kodinatan kungiyar a Najeriya Hadiza Dorayi ta ce kamata ya yi a ware wa mata tun suna yara kansu game da mahimmancin shigar da kara a duk lokacin da Wani ya ci zarafinsu.
Hadiza ta ce kungiyar na tallafawa mata sama da 200,000 da suka fita daga gidajen mazajen su saboda irin wannan matsaloli wajen ganin sun samu ilimin boko domin samun aikin yi.
Ta ce mata kowace mace za ta iya fita daga auren da ake cin zarafin ta inda bata raina kanta ba.
Hadiza ta ce kungiyar su na kokari wajen wayar da kan matan dake fama da matsala irin haka a auren su.
Ta ce idan mace ta amince ta fita daga gidan mijinta kungiyar ta na horar da mata sana’o’in hannu domin su fara cin gashin kansu.
Hadiza ta ce kungiyar na aiki a jihohi 10 kuma ta gina gidaje da dama domin kula da matan da suka baro gidajen mazajen su.
Discussion about this post