Shugaba Muhammadu Buhari ya yi wa Gwamnan Imo Hope Uzodinma, Ministan Makamashi Abubakar Aliyu kiran gaggawa dangane da matsalolin da su ka addabi ƙasar nan.
Error: Contact form not found.
Ba a kan su gayyatar gaggawar ta tsaya ba, an kuma gayyaci Mashawarcin Shugaban Ƙasa a Ɓangaren Tattalin Arziki, Doyin Salami.
Dukkan su dai sun gana da Buhari ɗaya bayan ɗaya, a tare ba.
Buhari ya gayyaci Ozodinma na Imo domin tattauna yawaita da munin tashe-tashen hankula a jihar, inda a baya-bayan nan aka kai hari gidan Shugaban Kungiyar Kishin Ƙabilar Igbo Zalla, Ndigbo George Obiozor, har aka ƙone kadarori da dukiya mai tarin yawa.
An gayyaci Ministan Makamashi ne sanadiyyar gagarimar matsalar wutar lantarki wadda ke neman durƙusar sa harkoki a ƙasar nan.
Shi kuma Mashawarci kan Tattalin Arziki, an gayyace shi ne domin yin bayanin halin da ake ciki da kuma laluben mafita.
Premium Times ta buga rahoton cewa SERAP ta bai wa Gwamnatin Buhari wa’adin kwanaki bakwai kan matsalar lantarki, inda ta ce masa, “ya kamata ka cika alƙawarin da ka ɗauka ranar rantsar da kai, ka ce za ka binciki yadda kuɗaɗen gyaran wuta su ka salwanta,” amma shiru’ -SERAP ga Buhari
Ƙungiyar SERAP ta yi kira ga Shugaba Muhammadu Buhari cewa ya sa Ministan Shari’a Abubakar Malami da EFCC da ICPC su binciki masu hannu wajen kashe aƙalla Naira Tiriliyan 11 a ɓangaren gyaran wutar lantarki, tun daga 1999 har zuwa yau.
SERAP ta ce ba zai yiwu ƙasa kamar Najeriya ta riƙa kasancewa cikin duhu ba, amma a duk shekara wasu na danne biliyoyin nairorin da ake warewa da sunan gyaran matsalar wutar lantarki.
Wannan kira na SERAP ya zo ne daidai lokacin da Najeriya ke cikin wata gagarimar matsalar wutar lantarki, inda yawan wanda ake samu bai wuce wats 2200 ba.
Bugu da ƙari kuma tashoshin samar da hasken lantarki 14 a ƙasar nan duk sun durƙushe.
SERAP ta ce daga 1999 zuwa yau, an ragargaje zai kai naira tiriliyan 11, wuta ba ta gyaru ba, sannan babu kuɗaɗen babu alamar su, an yi biyu-babu kenan.
Kan haka ne SERAP ta ce a gaggauta yin bincike, a kamo, a gurfanar kuma a ɗaure duk wanda aka samu da laifin karkatar da kuɗaɗen aikin gyaran wuta ko wane ne. Sannan kuma a taka cikin sa sai ya amayar da kuɗaɗen da ya karkatar.
Wannan wasiƙa dai SERAP ta aika wa Buhari ita a ranar 19 Ga Maris, mai ɗauke da sa hannun Mataimakin Daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare.
“An shafe shekaru masu ‘yawa ana yi mana ‘yar-burum-burum kan aikin gyaran wutar lantarki a ƙasar nan.
“SERAP na runatar da Buhari cewa sai ka cika alƙawarin da ka ɗauka a ranar rantsar da kai, 29 Ga Mayu, 2015, sannan wuta za ta gyaru.
Matsalar Lantarki: Alƙawarin Buhari A Ranar Rantsar Da Shi:
“Babban abin kunya ne a ce kamar Najeriya ƙasa mai sama da mutum miliyan 180 amma ba su iya samun wutar da ta wuce miga wats 4000. Ba za
mu taɓa barin haka ya ci gaba ba.” Inji Buhari a cikin jawabin sa a 2015.
Sannan kuma SERAP ta nemi Buhari ya bi umarnin kotu wanda Mai Shari’a Austine Chuke Obiozor ya umarci Gwamnantin Tarayya tun a cikin 2019 cewa ta fallasa sunayen waɗanda su ka ci kuɗaɗen gyaran wutar lantarki, sunayen kamfanoni da adadin kuɗin da kowa ya salwantar.
Discussion about this post