Ministan Shari’a kuma Antoni Janar Abubakar Malami, ya bayar da dalilan da su ka sa zai tura dakataccen Mataimakin Kwamishinan ‘Yan Sanda Abba Kyari zuwa Amurka, domin ya fuskanci tuhumar da ake yi masa tare da mazambaci Hushpuppi.
Malami ya bayar da dalilan sa a cikin wata sanarwa da Kakakin Yaɗa Labaran sa Umar Gwandu ya raba wa manema labarai a ranar Alhamis.
Ya ce Malami ya aika sa takardar sanar da tura Kyari Amurka ne a Babbar Kotun Tarayya, Abuja.
A ranar Alhamis ce labari ya bazu cewa Malami ya aika da sanarwar neman sahalewar Babbar Kotun Tarayya cewa Antoni Janar ɗin zai tura Kyari Amurka ya fuskanci tuhuma.
Dalilan Minista Malami Na Shirin Tasa Ƙeyar Kyari Amurka:
“Kamar yadda ku ka sani, matakai da sharuɗɗan aika wanda ake zargi zuwa wata ƙasa, lamari ne da ke shafar ababe da dama.” Inji Malami.
Ya ƙara da cewa ya aika wa Babbar Kotun Tarayya neman amincewa a tura Kyari Amurka, bayan da Amurka ɗin da kan ta ta nemi hakan.
“Akwai sabubba da matakai na ƙasa-da-ƙasa, na cikin gida da kuma na fannin shari’a.
“”Matakin farko shi ne ba a maganar aika wanda ake zargi zuwa ƙasar da ya yi wa laifin, har sai ita ƙasar ce ta aiko wasiƙar neman a tura mata shi domin ta hukunta shi.
“Ofishin Antoni Janar kuma Ministan Shari’a ya karɓi wannan wasiƙar roƙon a tura Kyari zuwa Amurka, daga ita Amirka ɗin.” Inji sanarwar.
Gwandu ya ƙara da cewa bayan Ofishin Minista ya karɓi wasiƙar Amurka, ya yi nazarin ta kuma ya bi diddigin lamarin kafin ya kai ga aika wa Babbar Kotun Tarayya sanarwar za a tura Kyari Amurka. “An tura wasiƙar ga hukumomin da lamarin ya rataya a kan su, domin ɗaukar matakin da ya zama tilas a ɗauka.” Cewar sanarwar.
Bisa tsarin dokar Najeriya, Babbar Kotun Tarayya ke bada odar a tura mutumin da wata ƙasa ke tuhuma zuwa ƙasar da ke tuhumar sa ɗin.
Sai dai kuma a kan ƙalubalanci umarnin turawar har zuwa matakin Kotun Ƙoli.
Tsalle Ɗaya Ke Jefa Mutum Rijiya:
Mu Na Da Hujjojin Damƙa Abba Kyari Ga Mahukuntan Amurka, Inji Minista Malami:
Satin farko na watan Fabrairu ne, Antoni Janar na Tarayya, kuma Ministan Shari’a Abubakar Malami, ya bayyana cewa akwai ƙwararan dalilan da za su sa a ci gaba da binciken Abba Kyari, dakataccen ɗan sandan da aka zarga da hannu a harƙalla da damfara tare da babban ɗan damfara, Hushpuppi.
Malami ya yi wannan ƙarin bayanin a ranar Litinin, lokacin da ya ke amsa tambayoyi ga Gidan Talabijin na Channels, a Abuja.
A cikin watan Yuli ne Gwamnatin Amurka ta fallasa zarge-zargen da ta ke yi wa Kyari da sauran abokan harƙallar sa.
Ramon Abbass dai da aka fi sani da Hushpuppi, ɗan Najeriya ne da mahukuntan Amurka suka damƙe a Dubai cikin watan Yuni, 2020. Tuni ya amsa laifin sa, kuma cikin wannan shekarar ce za a yanke masa hukunci.
Bayan mahukuntan Amurka sun nemi Najeriya ta ba su Abba Kyari domin ta tuhume shi, an dakatar da shi kuma ‘yan sanda suka kafa kwamitin bincike.
Sai dai kuma sun yi gum da bakin su, duk kuwa da cewa mutane na ta kururuwar a fito da sakamakon binciken a fili.
Amma kuma yanzu Malami wanda ofishin sa ne ‘yan sanda suka aika da sakamakon rahoton binciken da aka yi wa Kyari, a ranar Litinin ya tabbatar cewa “akwai hujjojin da za su sa ko dai a ci gaba da gurfanar da Kyari, ko kuma a aika shi ga mahukuntan Amurka, inda ake jiran a kai shi a tuhume shi.
Da aka tambayi Malami ko kwamiti ya kama Kyari da laifi, sai ya ce, “ai kwamiti ba zai kama wanda ya ke bincike da laifi ba. Sai dai ya fito da wasu hujjojin da za a iya amfani da su a matsayin abin dogaro kan zargin da zai kai ga gurfanar da mutum a kotu. A kotu ne za a iya kama shi da laifi, ta hanyar amfani da hujjojin da masu bincike su ka gabatar.”
Malami ya ce dalili kenan da ya da muke da wasu hujjojin da suka sa ake zargin sa.
Discussion about this post