PREMIUM TIMES ta buga labarin cewa ‘yan bindiga sun kashe mutum 30 inda kashi 80% daga cikin su jami’an tsaro ne a makon jiya a kasar nan.
Daga cikin jami’an tsaro 24 din da aka kashe akwai ‘yan sanda 18 da sojoji shida.
Kudu maso Gabas
‘Yan bindiga sun kashe jami’in hukumar NDLEA a harin da suka kai ofishin hukumar dake jihar Ebonyi ranar Talata.
A harin da ‘yan bindigan suka kai da karfe biyun dare ‘yan bindigan sun kashe wani mutum daya.
Bayan haka a ranar Laraba sun kashe jami’an hukuma firzin biyu dake sintirin aiki a garin Okigwe.
Daga nan ‘yan bindigan sun tada bam a ofishin ‘yan sanda dake Umuguma a karamar hukumar Owerri ta Yamma inda suka kashe ‘yan sanda biyu dake aiki a wannan rana.
Arewa maso Yamma
‘Yan bindiga sun kashe mutane uku da ‘yan sanda 10 a garin Ngaski da Gafara dake karamar hukumar Ngaski a jihar Kebbi.
Arewa ta Tsakiya
A hari da ‘yan bindiga suka kai garin Nasko dake karamar hukumar Magama ‘yan bindiga sun kashe dan sanda daya a ofishin ‘yan sandan dake garin.
Kakakin rundunar Wasiu Abiodun ya ce Mohammed Umar ya gamu da ajalinsa ne a artabu da suka yi da ƴan bindiga ayan batakashi da suka yi da yai sanadiyyar rayukan wasu ‘yan sanda biyu da ‘yan sa kai hudu.
Bayan haka a jihar Neja ne sifeton ‘yan sanda ɗaya ya rasa ransa a Kauyen Bangi dake karamar hukumar Mariga.
Arewa maso Gabas
‘Yan kungiyan ISWAP sun kashe wani soja mai suna Jamilu.
Jamilu Wanda ya fara aiki da rundunar sojin Najeriya a shekaran 2021 ya rasu yayin da ISWAP suka kai wa sansanin sojoji hari dake Bama a jihar Borno.
Discussion about this post