A ci gaba da shari’ar tsohon Shugaban Hukumar NECO da JAMB, Dibu Ojerinde da ake yi, wani mai bada shaida wanda Hukumar ICPC ta gabatar a kotu, ya shaida wa Mai Shari’a yadda Ojerinde ya mallaki manyan kamfanoni da maka-makan gidaje, daga cikin naira biliyan ɗin da ake tuhumar su salwanta a hannun sa.
Wannan mai bayar da shaida na farko dai ya fara bayar da shaidar sa, yayin da ƙoƙarin daidaitawa ta hanyar ‘plea bargain’ ba ta yiwu ba.
‘Plea bargain’ shi ne ɓarawon gwamnati ya amince ya saci kuɗin, kuma zai mayar da su. Saboda haka kotu za ta yi masa sassaucin hukunci.
An dai yi ƙoƙarin wannan tattauna batun ‘plea bargain’ a ranar Laraba.
Mai Gabatar da ƙara ya shaida wa Mai Shari’a a Babbar Kotun Tarayya ta Abuja cewa tsohon Rajistaran JAMB ya mallaki manyan kantama-kantaman kadarori na maka-makan gidaje da kanfanoni a lokacin da ya ke Rajistara na JAMB.
Peter Oyewole, wanda garin su ɗaya da Ojerinde, ya shaida wa kotu cewa ya yi aiki ƙarƙashin Ojerinde a matsayin lauyan sa. Ya ci gaba da bayar da shaida kan abin da ya san Ojerinde ya saya da naira biliyan 5.2 ɗin da ake tuhumar sa da sacewa.
Tun a cikin watan Yuli 2021 ne ICPC ta gurfanar da shi kotu, inda ake tuhumar sa da laifuka 18 da suka ƙunshi satar naira biliyan 18.
ICPC ta ce ya saci kuɗin tun daga lokacin da ya ke Rajistara na NECO har zuwa lokacin da ya ke Shugaban JAMB.
Idan ba a manta ba, cikin watan Afrilu 2020, PREMIUM TIMES Hausa ta buga cewa ICPC ta ƙwace kadarorin biliyoyin nairori daga hannun Ojerinde, waɗanda suka haɗa da makarantu masu zaman kan su, gidajen mai, gidaje a jihohin Kwara da Oyo, waɗanda ya mallaka ta hannun ‘yan-kore a Ilorin, Ibadan da Ogbomoso.
Akwai kuma wasu a Ile Ife a Jihar Osun da kuma Abuja.
A ranar Talata Ojerinde ya nemi Kotu ta ɗage Shari’a zuwa kwana ɗaya, domin a ba shi damar ƙulla yarjejeniyar ‘plea bargain’.
Sai dai kuma an ci gaba da shari’ar a ranar Laraba, yayin da lauyan ICPC Ebenezer Shogunle ya sanar wa kotu cewa yarjejeniyar ba ta yiwu ba.
Daga nan ne Oyewole ya ci gaba da shaida wa kotu yadda shi da Ojerinde suka riƙa kafa kamfanoni da kuma sayen manyan kadarori na shi Ojerinde ɗin, a lokacin ya na Rajistaran NECO da kuma Shugaban JAMB, shi kuma Oyewole ya na lauyan sa.
Ya ce baya ga kamfanoni takwas da manyan gidaje da gidajen mai, har tulin hannayen jari Ojerinde ya saya a bankuna.
Za a ci gaba da shari’ar a ranakun 4 da 5 Ga Afrilu, bayan an damƙa wa kotu kwafe-kwafen takardun shaidu na rasiɗai da satifiket na shaidun mallakar kadarori a lokacin gabatar da shaidar.
Discussion about this post