• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Tambuwal and Atiku

    FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Tambuwal and Atiku

    FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba  sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    An yi amfani da ƴan daba ne aka kada ni – Bashir Ahmed

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    Da Ɗan bindiga da ‘Deliget’, Ɗanjuma ne da Ɗanjummai – Shehu Sani

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    ZAƁEN FIDDA GWANI: Fintirin Adamawa, Kashim ɗin Bauchi, Uban Makurɗi, Abachan Kano, Ashirun Kaduna sun yi nasara zaɓe na Jam’iyyar PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    Peter Obi ya fice daga PDP

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    TATTAUNAWA DA SARAKI:’Idan na zama shugaban ƙasa zan magance aringizon kuɗaɗen da ake yi wajen bayar da kwangiloli’

    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SARƘA UWAR RIKICI: Yadda rigingimu suka yi wa APC tarnaƙi da dabaibayin wahalar tsallake siraɗin 2023

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
February 4, 2022
in Babban Labari
0
ZAƁEN 2023: APC za ta iya faɗuwa zaɓe idan ba ta tashi tsaye ba -Buhari

Masu nazarin siyasa da masu jefa ƙuri’a baki ɗaya, sun yi tunanin jam’iyyar APC za ta kame kan ta daga irin zubar da kima da mutuncin da PDP ta yi, har ta rasa mulki bayan shafe shekaru 16 a jere.

Rigingimu su keta PDP cikin 2006 da kuma 2014, waɗanda su ka ja mata asarar mulki, lamarin da har yau APC ba ta daina yi mata bi-ta-da-ƙulli ba, tun bayan faɗuwa zaɓe cikin 2015.

Shekaru bakwai ɗin da PDP ta yi zuwa yau ta kasa kimtsa kan ta. Daga yau ta yi wawan-zama a tsakiyar kasuwa kowa na kallon al’aurar ta, gobe kuma sai ta ɗibga tulin abin kunya, ta yi sata gidan surukan ta. Ki kuma ka ga dangin uwar APC sun kaure faɗa tsakanin su da dangin uba.

APC wadda auren gamin-gambizar ACN, CPC, ANPP da APGA ne suka haife ta, shugaban ta na farko shi ne Bisi Akande.

Tun a ranar 6 Ga Fabrairu, 2013 aka fara batun yin gambiza, amma sai bayan wata biyar aka yi mata rajista, a ranar 31 Ga Yuli, ,2013. Daga nan ta yi mulki a 2015 , sannan ta sake lashe zaɓe a 2019.

Shekaru 9 bayan kafa APC, wannan jam’iyya mai mulkin ƙasa mai yawan al’umma miliyan 200, ta shiga rikici, ta afka cikin gararin da ke neman gagarar ta sasantawa.

Tun bayan sauke Adams Oshiomhole daga shugabanci APC ba ta sake zama lafiya ba. Dama kuma cutar amai da gudawar da jam’iyyar ta yi fama da shi ne a ƙarƙashin shugabancin Oshiomhole ya sa aka cire shi.

An naɗa Shugabannin Kwamitin Riƙo na Mutum 13, a ranar 25 Ga Yuni, ƙarƙashin Gwamna Mala Buni na Jihar Yobe. Aka ɗora masa alhakin shirya taron gangami ƙasa, cikin watanni shida. Amma har yanzu fiye da shekara ɗaya kenan, Buni ya kasa gudanar da taron gangami.

Hakan ya sa gwamnonin APC yin taro a cikin Nuwamba, 2021 a Abuja suka aza rana cewa za a yi gangami a cikin Fabrairu, 2022.

Hasalallun ‘Yan APC Sun Maka Jam’iyya Kotu, Su Na Ƙalubalantar Gangamin Fabrairu Da Shugabancin Mala Buni:

Tunanin da jam’iyyar APC ke yi na shirya gangamin taron ƙasa na neman samun cikas, yayin da wasu mambobin jam’iyya da aka ɓata wa rai sun maka uwar jam’iyya kotu, domin buƙatar a dakatar da taron.

Wata ƙarar kuma wadda wani hasalallen ɗan jam’iyya ya shigar, shi kuma ya nemi kotu ta gaggauta tsige Gwamnan Yobe Mai Mala Buni daga shugabancin jam’iyya na riƙon-ƙwarya.

Mutanen biyu duk sun shigar da ƙarar ce a Babbar Kotun Tarayya, Abuja, tsakanin watan Disamba 2021 zuwa Janairu 2022.

A ƙarar neman hana shirya taron wadda gungun wasu mutane biyar suka shigar, sun maka Mala Buni ne a kotu, tare da Hukumar Zaɓe Mai Zaman Kanta ta Ƙasa, INEC.

Hasalallun da su ka shigar da ƙara sun haɗa da Suleiman Usman, Mohammed Shehu, Samaila Isahaƙa, Idris Isah da Audu Emmanuel.

Ƙarar wadda aka shigar a ranar 4 Ga Janairu, sun nemi kotu ta dakatar da gangamin taron ƙasa da ake shirin yi a cikin Fabrairu.

Tuni gwamnonin APC sun shirya taro tsakanin Asabar da Lahadi, a Gidan Gwamnatin Jihar Kebbi, a Abuja.

Dama an daɗe ana neman a canja ranar shirya taron.

Cikin ƙara mai lamba FHC/ABJ/CS/3/2022, masu shigar da ƙara ta hannun lauyan su sun shaida wa kotu cewa su na so a dakatar da taron kuma kada a zaben shugabannin jam’iyya na ƙasa, saboda ba a kammala ko ba a yi zaɓen fidda gwani a wasu jihohi ba.

Sun nemi kada APC ta shirya zaɓen shugabannin jam’iyya a ranar gangami har sai ta fara shirya zaɓen wasu jihohi da da suka haɗa da Anambra da Zamfara tukunna.

Kuma sun nemi kotu ta hana INEC bayar da izni APC ta yi zaɓen shugabanni na ƙasa, ba tare da an yi na sauran jihohin da ba a yi ba.

Shugaban Matasan APC Ya Maka Mala Buni Da INEC Kotu:

Shugaban Matasan APC na Ƙasa, Zahraddeen Audu ya maka Mala Buni kotu, inda ya ƙalubalanci shugabancin sa a cikin APC.

Ya nemi kotu ta umarci Buni ya daina kiran kan sa shugaban jam’iyyar APC na Riƙo.

Ya shigar da ƙara a ranar 10 Ga Disamba, 2021, inda ya ce a matsayin Mala Buni na Gwamnan Jihar Yobe, tsarin mulki ya hana shi riƙe wani muƙami daban.

Gargaɗin Minista Keyamo: Mala Buni Haramtaccen Shugaban Jam’iyya Ne:

Farkon watan Satumba ne Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Festus Keyamo ya yi kakkausan gargaɗin cewa mulki zai iya suɓucewa daga hannun APC, idan Gwamna Buni ya ci gaba da shugabancin jam’iyyar ko na tsawon sati ɗaya ne.

Ƙaramin Ministan Ƙwadago, Festus Keyamo, ya gargaɗi jam’iyyar APC cewa akwai gagarimar matsalar da ta tunkari jam’iyyar, matsawar Gwamna Mai Mala-Buni na Jihar Yobe ya ci gaba da kasancewa Shugaban Jam’iyya na Riƙo har zuwa jibi Asabar, ranar zaɓe shugabannin APC a matakan Kananan Hukumomi da Jihohi da za’a yi ranar 31 Ga Yuli.

Yayin da ya aika da wata wasiƙar gaggawa ga jam’iyya s asirce, wadda ta faɗo hannun PREMIUM TIMES, Keyamo wanda shi ma gogaggen lauya ne, ya bayyana haramcin riƙe APC da Gwamna Buni ke yi, domin Dokar Ƙasa da Dokar APC sun haramta Gwamna ya riƙe wani muƙami ko shugabanci banda na gwamna da aka rantsar da shi don ya riƙe.

Wannan mahaukaciyar guguwa ta taso ne sanadiyyar hukuncin da Kotun Ƙoli ta Yanke, inda ta jaddada nasarar Gwamna Rotimi Akeredolu na Ondo, na APC, kan Eyitayo Jegede na PDP.

Yadda Sakacin Lauyoyin Jegede Ya Bai Wa Akeredolu Nasara A Ɓagas:

Keyamo ya ce Jegede ɗan takarar PDP ya shigar da Gwamna Akeredolu ƙara, bisa zargin zaɓen da bai cancanta ba, domin a lokacin da aka yi zaɓen cikin Oktoba 2020, Gwamna Mala Buni ne Shugaban Riƙon APC, wanda haramun ne a Dokar Ƙasa Sashe na 183 na 1999 Gwamna ya riƙe wani muƙami daban da na Gwamna.

Haka ma Dokar APC Sashe na 17 ya haramta wa Gwamna riƙe wani muƙami lokacin da ya ke kan mulki.

“Inda Jegede da lauyoyin sa su ka kwafsa shi ne da ba su haɗa da sunan Gwamna Mala Buni Shugaban Riƙon APC tare da na Gwamna Rotimi sun maka su kotu tare ba.

“Da an haɗa da sunan Shugaban Riƙon APC, to da a ranar Litinin Kotun Koli ta soke zaɓen ta bai wa Jegede na PDP nasara.” Inji Keyamo.

A kan haka ne Keyamo ya bada shawarar cewa lallai kamata ya yi a ɗage zaɓen shugabannin APC na Ƙananan Hukumomi da na Jihohi da aka shirya gudanarwa a ranar Asabar mai zuwa.

“Domin banda Mai Mala-Buni, akwai Gwamnonin Osun da na Neja a cikin Kwamitin Amintattun APC, waɗanda su ma bai kamata a saka su a ciki ba.

Ya ce idan aka yi zaɓen shugabannin jam’iyya a ƙarƙashin Buni, to duk wanda ya ci zaɓe a ƙarƙashin APC, tun daga kan kansila har shugaban ƙasa sai kotu ta ƙwace kujerar sa.

A kan haka ne ya bada shawara a ɗage zaɓe na shugabannin ƙananan hukumomi da na Jihohi. Sannan a gaggauta cire Mala Buni, ta hanyar taron Majalisar Zartaswar APC na gaggawa, wanda zai cire waɗannan shugabannin riƙo, ya naɗa wasu.

Gwamna Rotimi ya tsallake rijiya ne saboda Alƙalai huɗu daga cikin bakwai ne su ka yarda da zaɓen sa bisa dalilin cewa sun yarda Gwamna Buni bai cancanci riƙe jam’iyya ba, amma mai ƙara fa bai shigar da Buni a cikin ƙarar da ya shigar ba.

Sauran lauyoyi uku kuwa su ka ce ba sai an sha wahalar shigar da sunan Buni ba, tunda dai bai cancanci shugabancin APC ba, to Gwamna Rotimi bai ci zaɓe ba ƙarƙashin APC kenan.

A kan haka ne Keyamo ya ce wannan shari’a ta nuna kenan duk wanda zai kai ƙarar APC nan gaba, to matsawar ya haɗa da sunan Buni, ko tantama babu nasara zai yi a kotu.

Taron Gangamin Da APC Za Ta Yi A Ranar 26 Ga Fabrairu, 2022:

Yanzu dai ta tabbata APC za ta yi gangami a ranar 26 Ga Fabrairu, a Abuja. Mala Buni da Shugaban Gwamnonin APC Kayode Fayemi duk sun tabbatar da haka. Sai dai kuma tabbas akwai rikici, domin ko a kwanan nan sai da Babban Daraktan Ƙungiyar Gwamnonin APC ya ajiye aiki, bisa abin da ya kira sakin hanya madaidaiciya da APC ta yi.

Baya ga irin su Minista Keyamo masu nuna haramcin shugabanincin Buni da irin illar da zai haifar wa APC nan gaba a kotu, ita ma jam’iyyar PDP ta nemi a tsige shi, ta ce haramtacce ne.

Akwai masu raɗe-raɗin cewa Buni ya maƙale kan kujerar APC don ya ci gaba da yaɗa manufofin sa na neman zama mataimakin shugaban ƙasa, idan aka miƙa takarar mataimaki ga yankin Arewa maso Gabas.

Shi kuma Sakataren APC John Akpanudoedehe an ce ya maƙale ne saboda ya na son tsayawa takarar gwamna a jihar sa Akwa Ibom.

Rigingimun APC A Jihohi 16:

Yayin da gangamin watan Fabrairu ya ƙarato, a lokacin kuma APC na fama da rikicin shugabanci na jiha a jihohi 16 da suka haɗa da Zamfara, Kano, Abia, Kwara, Osun, Delta da Cross Riba. Sai kuma Ogun, Oyo, Akwa Ibom, Kebbi, Ribas, Legas, Enugu, Imo da Ekiti.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga labaran ƙaƙudubar rikicin APC a Kano, inda shugabancin jam’iyya ya suɓuce daga hannun su Gwamna Abdullahi Ganduje. Ta kuma sha buga rikicin jihar Kwara, inda inda Gwamna da Ministan Yaɗa Labarai Lai Mohammed suka keta fatarin APC gida biyu, kowa ya keci tsagi ɗaya.

Rikicin baya-bayan nan shi ne na Jihar Kebbi, inda APC ta rikice daga sama har ƙasa, saboda zargin ƙoƙarin da Gwamna Abubakar Bagudu ke yi don ya ɗora Ministan Shari’a Abubakar Malami ya zama ‘halifan sa.’

Wannan ya haifar da rikici tsakanin Sanatocin APC, su Adamu Aliero da kuma Gwamna Bagudu.

A Jihar Gombe, sai dai a ce har yanzu ta-ciki na ciki, tsakanin ɓangaren Gwamna Inuwa Yahaya da ɓangaren Sanata Ɗanjuma Goje.

Duk da an shirya bayan yaƙin da ya haddasa asarar rayuka a tsakanin su, ana ganin har yau akwai sauran rina a kaba.

Da alama dai Kwamitin Sasantawar da jagoran APC Bola Tinubu ya jagoranta cikin 2018, har aka samu aka sake lashe zaɓen 2019 ko dai akwai sauran aiki a gaban sa, ko kuma akwai buƙatar sake kafa wani irin sa, domin ya kashe wutar da ke cin tulin tsintsiyar APC.

Saboda matsawar wutar ta ci gaba da ci, to APC za ta iya rasa tsintsiyar da za ta share masallaci, kasuwa ko tasha.

Tags: AbujaAPCBuhariHausaNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Dalilin da ya sa na fice daga PDP na koma APC – Sanata Bwacha

Next Post

ARZIKI DOLE: Yadda wasu matasa ƴan ƙasa da shekaru 20 suka kashe budurwarsu don su kuɗance

Next Post
ARZIKI DOLE: Yadda wasu matasa ƴan ƙasa da shekaru 20 suka kashe budurwarsu don su kuɗance

ARZIKI DOLE: Yadda wasu matasa ƴan ƙasa da shekaru 20 suka kashe budurwarsu don su kuɗance

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • ƘURUNƘUS: Atiku Abubakar ya lashe zaɓen fidda ɗan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar PDP
  • ZAƁEN FIDDA-GWANI: Cin hancin da ‘deliget’ za su karɓa a hannun ‘yan takara zai ƙasa dagula matsalolin da ƙasar nan ke fama da su -Sheikh Gumi
  • FIDDA-GWANIN PDP 2023: Tambuwal ya janye ya ce ya na bayan Atiku
  • IDO NA GANIN IDO: Dalilin baza jami’an mu filin zaɓen fidda-gwanin PDP a Abuja -EFCC
  • TURA TA KAI BANGO: Dalilin da ya sa dole na hakura da takarar sanatan Kebbi – Aliero

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.