Ko yan Nijeriya kuwa suna nazari game da cigaban da tabarbarewar ilimi ke fuskanta? A yau fa a Nijeriya lacewar ilima fa, tafi lalacewar harkar tsaro, kawai rashin tsaro kan dauke rayuwar mutane ne lokaci guda ba tare da sanin kowa ba, ko tarwatsa al’ummah ko duk masifar hakan kan kawo, wanda ita dole tana bukatar maganin na nan take. Amma fa in munyi dogon nazari, lalacewar ilimi daga matakin kananan makarantu zuwa jami’a, shi ya bada babbar gudunmawa wajen rusa kowanne fanni daga tattalin arzi, lafiya zuwa ita kanta harkar tsaron, uwa uba rasa ingantacciyar gudanar da mulkin al’ummah.
Makarantun gwamnati a ko wane mataki ba wai kawai jami’a ba a kowane lokaci sake lalacewa suke, kwari da nagartar ilimi a kowane mataki lalacewa yake, musamman a yankin arewacin Nijeriya.
Babban abin da ya kamata mu sake nazari a kayi shine, yau shiga makarantun gwamnati a kowane mataki, ya zama sai talaka kawai, ko kuma in ya zama dole ne kawai mutane ke kaiwa yaran su makarantun gwamnati.
A yau duk mai dama-dama daga yan kasuwa zuwa ma’aikata ba kowa ke kai dansa makarantar gwamnati ba, hatta a wasu wuraren ma Headmaster da malamai basa kai yayan su makarantar da suke koyarwa, su kan kaisu makarantun kudi, su kuma su koyar a makarantun gwamnati. Irin wannan halayya tana iya karuwa a manyan makarantun Nijeriya ganin yadda a kullum a ke bude makarantu masu zaman kansu.
Ko da yake zaiyi wahala a ga kananan makarantu na firamare da sakandare suna shiga yajin aiki kamar yadda a ke ganin malaman jami’oin Nijeriya ke yawon rufe makarantun su, su tafi yajin aiki, kamar yadda a yanzu suke shirye-shiryen shiga wani sabon yajin aiki.
A wannan karon kungiyar ASUU sun dauko sabon salo a bana, a yayin da ASUU suke ware rana guda a dukkanin jami’a wanda baza a yi karatu ba, dominsu fahimtar da dalibai da iyayen dalibai dama sauran al’ummah akan dalilin su na daukan matakin sai baba-tagani in har sun tsunduma wannan yajin aikin.
Kusan dalilan da kungiyar ASUU suka bada na daukar matakin shiga yajin aiki, bai wuce dalilan da ASUUn suke badawa a abaya ba, yayin da za su dauki irin wannan mataki.
A tawa fahimtar kwararen dalilan ASUU a wannan karon bai wuce Sabinta Yarjejeniyar ta da Gwamnati ba ta 2009 wato Renegotiation of 2009 Agreement, samar da kudade don gyaran Jam’ioin Nijeria da samar musu kayan aiki, wanda a yanzu kungiyar sunce suna bin gwamnatin tarayya naira biliyan 880 na revitalization of universities wato kudin gyaran makarantu da kuma kin amincewar kungiyar na shiga tsarin gwamnati na biyan albashi bai daya wato IPPS, yadda suka bakaci yin amafani da manhajar da suka kirkira wato UTAS.
Ko da yake a wani bangaren manazarta suna tausaya wa malaman jami’oi a Nijeriya musamman man ma yayin da aka yin misali da takwarorin su na kasashe makwabta, duk da cewar Nijeriya tafi wadannan kasashe karfin tattalin arziki, malaman jami’oin Nijeriya kusan sunfi kowa karancin albashi a yau, wanda kololuwar albashin Shehun Malami wato Professor bai wuce N400,000 da doriya ba, wanda wasu malaman ma basa karbar albashin da ya kai N130,000 ga kuma dibgin aiki na koyar wa saboda yawan daliban da suke jami’oin kasar. Dadi da kari ana bukatar wadannan Jami’oi suna fitowa da bincike a kowane fanni da za a gina kasar nan da shi.
A yarjejeniyar ASUU da Gwamnati ta 2009, ya kamata tun a shekara huda baya a ce an sake duba wannan tsarin albashin, a dalilin ASUU na sake shiga yajin aiki shine jan kafar da gwamnati take yi a kan wannan yarjejeniya da kuma kudurin gwamnati na sake maida duba ga tsarin albashin na su zuwa ga Tripartite Committee wato kwmitin da ya samar da sabon karancin albashi, wanda ASUU suke ganin kamar wasa ne da hankalin su gwamnati ta keyi musu, ganin tsawon lokacin da aka dauka akan batun kuma babu wani kwakkwaran mataki.
Kudaden da ake bawa malaman jami’a na AEA (Academic Earn Allowance) wato allowance din in-kayi-aiki-ka-samu da kuma Revitalizing Fund wato samar da kudi don gyaran makarantu, wanda ya hada da gyaran dakunan kwanan dalibai, dakunan koyon karatu, dakunan koyon kimiya wato laboratory da sauran kayan koyo da koyarwa. Duk da cewar gwamnati ta ce ta biya N5.5B na Earned Allowance da Revitalization Fund, amman ASUU sunce wannan ko kusa bai kai kudin da ake bukata ba gyaran Jami’oin Nijeriya.
A jayayyar ASUU da Gwamnati akan IPSS da UTAS, bisa nuna kin gamsuwar su da tsarin IPSS, wanda suka zayyano matsalolin da ke cikin tsarin ta re da samar da wata manhajar domin amfani da ita a Jami’oi. Bayan yajin aikin baya gwamnati ta aminta da karbar wannan Manhaja ta UTAS (University Transparency and Accountability Solution) bisa sharadin sai ta tsallake gwaje-gwaje na hukumomin Nijeriya. A bisa wannan dalilin ASUU na zargin gwamnatin da jan kafa a kan wannan manhaja.
Duk da kasancwar wasu da ga cikin bangarori na gwamanti da masu fada a ji sun sha shiga tsakanin ASUU da Gwamnati, ko da a yunkurin ASUUn na baya bayan nan Shugaban Majalissar Wakilai ya shiga tsakani a yayin da aka cimma yarjejeniya suka fasa shiga yajin aik, Shugabannin kungiyoyin addinai, ko a wannan karon ma gammaayar kungiyoyin addinai sun kaiwa Shugaba Buhari ziyara, kuma sun sanya baki a kan a samo karshen wannan matsala.
Amma, abin tambaya a ina matsalar ta ke? Shin lokaci baiyi ba da duk mai ruwa da tsaki a kan harkar ilimi da ma mashawartan gwamnati, da kuma ita gwamnatin kanta, da shugabbbannin siyasa da su samar da sahihiyar hanyar warware wannan matsala don inganta ilimin manyan makarantu a Nijeriya?
To fa in har ba a bi a tsinake ba, matsayin jami’oin gwamnati zai koma tamkar makarantun primary da sakandire na gwamnati, wanda karatu a ciki sai ya zama maka dole, wanda a karshe kasar a ke rusawa a hankali, wanda alamu na nunawa.
Ya kamata a yanzu tunanin mutane ya wuce karamin tunani na kawai irin matsalar da wannnan yajin zai hafar musamman a lokacin da aka shigo kakar siyasa da zabe. Ya kamata a rinka kallan wannan matsala a matsayin babbar matsala da take da bukatar kawo karshen ta na har abada, domin ilimin matasa shine ruhi da dogaran kasar nan don ci gaba a nan gaba.
alhajilallah@gmail.com
Discussion about this post