Zargi: Wani labari da aka yi ta yadawa a whatsapp na zargin wai mahukunta a NYSC sun dakatar da albashin masu yi wa kasa hidima na watan Janairun 2022 zuwa wani lokaci.
Ranar 27 ga watan Janairun 2022 mutane da dama suka rika yada wani labarin da jaridar Vanguard ta wallafa mai nuna cewa wai hukumar NYSC ta dakatar da albashin wadanda ke yi wa kasa hidima zuwa wani lokaci nan gaba.
Wannan zargi wanda yawancin wadanda suka gani a Whatsapp ne ya ce: ” An dakatar da albashin wata-wata na dalibai dake yi wa kasa hidima (NYSC) na watan Janairun 2022 zuwa wani lokaci nan gaba“.
Hukumar NYSC na biyan dalibai masu yi wa kasa hidima alawus din naira N33,000 duk wata. Sai dai wannan labarin ya kawo rudani da fargaba a tsakanin dalibai ganin kila shikenan ba za su samu alawus din ba a karshen wanna wata.
Omobolanle Kamarudeen daya daga cikin masu yi wa kasa hidima a jihar Oyo ta ce a ganinta labarin gaskiya ne tunda har yanzu bata samu alawus dinta na wannan wata ba.
” Yau 27 ga watan Janairu kuma ba su biya mu ba. Na fara tsoron ko labarin gaskiya ne”.
Ita ma AnjolaOluwa Omotoshi wadda ke na ta bautar kasa a jihar Ogun ta fadawa Dubawa cewa ita ma da saka dakatar da alawus din da Vanguard ta yi a shafinta.
Ta ce “ Ni ma na gani ne a shafin wata kawa ta sai na dauka gaskiya ne, sai na saka a shafina toh, kuma gashi har yanzu ba a biya mu alawus ba”.
Tantance gaskiyar maganar
Dubawa ta fara da zuwa shafin jaridar Vanguard dan ganin ko akwai wani labari dangane da dakatar da albashin masu bautar kasa NYSC. Sai dai ko daya babu wani labari makamancin haka. Daga nan, sai Dubawa ta tuntubi editan sashen labaran yanar gizo na Vanguard, Victor Ogunyinka wanda ya tabbatar cewa jaridar vanguard bata wallafa wani labari game da albashin NYSC ba.
Ogunyinka ya ce bayan da muka tuntube shi ya koma ya binciki babban kundin labaransu kuma bai ga wani abu makamancin haka ba.
” Ina iya tabbatar muku cewa ba wani labari haka a shafin mu, ya ce. Labarin karshe da muka yi dangane da NYSC ranar 23 ga watan Janairu muka wallafa kuma ya danganci kudurin dokar samar da gidauniya/asusun amincewa.
“ Na duba babban shafinmu da na kananan labarai wanda da mukan yi, ba abin da ya yi kama da haka, ba daga wurinmu ba ne”.
Mai magana da yawun NYSC Emeka Mgbemena, shi ma ya karyata labarin. Ba gaskiya ba ne. Ku yi watsi da wannan magana. Wasu ne kawai masu neman tada zaune tsaye da kawo rudani a tsakanin mutane kawai.
A Karshe
Batun dakatar da albashin dalibai masu bautar kasa NYSC na watan Janairun 2022, ba gaskiya ba ne. NYSC ta karyata labarin ta kuma nisanta kanta da shi. Ita ma jaridar Vanguard ta ce ba ita ta rubuta labarin ba kamar yadda ake ta yadawa.
Discussion about this post