Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya aika da sakon jinjina da yabo ga gwamnan jihar Kaduna Nasir El-Rufai bisa ayyukan raya jiha da yayi a jihar Kaduna.
Shugaba Buhari ya ce bayyana haka ne da yake karbar bakuntan mataimakiyar gwamnan Kaduna Hadiza Balarabe da sarkin Zazzau Nuhu Bamalli a fadan shugaban Kasa ranar Laraba.
Buhari ya ce El-Rufai yayi abin a yaba a jihar Kaduna. ” Gwamna El-Rufai ya canja fasalin jihar da kantamakantaman ayyukan da ba a taɓa irinsu ba. Idan ka shiga Kaduna sai ka haɗa da na’ura kafin ka gane wasu wuraren in ba haka ba zaka bace bat.
” Ina so ku mika masa gaisuwa ta ta musamman.”
Dalilin da ya sa mu ka maida hankali wajen gina ayyukan raya ƙasa
Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana cewa gwamnatin sa ta bazama wajen bayar da fifikon gina ayyukan raya ƙasa ne a faɗin Najeriya, domin sauƙaƙe wa jama’a ƙuncin rayuwar da su ke ciki.
Buhari ya yi wannan bayanin a ranar Talata a Abuja, lokacin da ya karɓi baƙuncin wata tawagar da ta kai masa ziyara daga Jihar Kaduna, a ƙarƙashin jagorancin Sarkin Zazzau, Ahmed Bamalli da kuma Mataimakiyar Gwamnan Kaduna, Hadiza Balarabe.
Ya ce tunda aka kammala aikin titin mota da na jirgin ƙasa daga Legas zuwa Ibadan, lamarin zirga-zirga ya bunƙasa sosai.
“Ni dama manufofi na a bayyane su ke, duk da ƙarancin kuɗaɗen shigar da Najeriya ke samu, na sha alwashin magance matsalar rashin gina ayyukan inganta ƙasa da ba a kula da su can a baya ba.
“Idan muka dubi tarihin yadda ƙasashe suka ci gaba, su ka bunƙasa a duniya, za mu ga kowace a cikin su sai da ta inganta ayyukan raya ƙasa sannan ya haye matakin ci gaba.
“A da muna da titinan jiragen ƙasa. Mutanen kudancin Kaduna za su iya tuna wannan.
“Wace ƙasa ce za ta iya ci gaba ba tare da ta inganta titinan ta ba na motoci da titinan jiragen ƙasa da wutar lantarki? Dalili kenan na yi tunanin gara na magance matsalar kayan inganta ƙasa.
“Na san ‘yan Najeriya akwai don gasar rige-rigen harkokin kasuwanci. To idan aka gyara titinan motoci, na jiragen ƙasa da makamashi kuwa, harkokin kasuwancin ƙaruwar zai yi sosai.” Inji Buhari.
Buhari ya tabbatar masu da cewa za a ci gaba da samar da ayyukan raya ƙasa, ciki har da aikin ginin tagwayen titinan Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano, wanda kamfanin Julius Berger ke kan aikin ginawa.
Discussion about this post