Zargi: Wani mai amfani da shafin Tiwita ya wallafa bidiyon da ke zargin wai Najeriya na tasa keyar baki masu son zuba jari a kasar.
Kalmar „Xenophobic” wanda ke nufin kyamar baki na tashe kuma a duniyar gizo musamman a shafin Tiwita. Kamar yadda aka saba kasashen da abun ya shafa su ne Najeriya da Afirka ta Kudu. Sai dai a wannan karon labarin ba shi da tushen kamawa, akwai zarge-zarge kala-kala marasa kan gado. Wani mai amfani da shafin na Tiwita, dan Afirka ta Kudu ya sanya bidiyon da ke zargin wai ‘yan Najeriya na koran baki wadanda ke da niyyar zuba jari a kasar.
Mutane sama da dubu tara (9) sun kalla, mutane dubu 400 sun yi ma’amala da labarin. Lamarin dai ya janyo mahawara tsakanin mutane amma babu wanda ya amince da batun wariyar.
Agboola Ayobami (@AYOMITAN_1) ya ce abubuwan da ke cikin bidiyon ba daga Najeriya ba ne “daga gani ka san wannan bidiyon ba Najeriya ba ne, amma mutane saboda son zuciya bai barin mutane su kalli bidiyon da kyau.”
Wani mai amfani da shafin (@Thobho5) shi kuma tambya ya yi: “Idan ba ‘yan Najeriya ba ne su waye? Sai ku fadakar da mu.”
To amma me bidiyon ke cewa?
Bidiyon ya nuna wani mutun ya na jawabi a wani taro, yana cewa ya kamata baki su bar kasuwanni. Mutumin ya ce „GEDA na so ta sanar cewa wa’adin da muka baiwa baki a kasuwanninmu ya cika dan haka mu na so su tashi su rufe shagunansu.“ Bidiyon mai tsawon dakiku 45 bai bayyana takamaiman kasar da aka yi bidiyon ba, ko ma bakin da ake yi da su.
Sai dai daga cikin wadanda su ka yi tsokaci wasu sun ce Ghana ne ba Najeriya ba.
„Ghana ne ba Najeriya ba, me ya sa kuke tunanin wai Najeriya za ta yi wa baki haka? Yaya za su yi? In ji Bafflord (@BhadmosLukman)
Tasirin da wannan zargin zai iya yi
A shafin Tiwita da sauran kafofin sadarwa na soshiyal mediya, akwai rashin jituwa tsakanin Najeriya da Afirka ta Kudu. Yayin da ake wa wannan zargin kallon maganar fatan baki zai iya kasancewa babban matsala. Na farko, zai iya ta’azara rikicin da ke tsakanin kasashen biyu har ma ya haddasa tashin hankali. Na biyu zai iya bata dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu.
Tantancewa: Gano gaskiya
Sadda Dubawa ta yi nazarin bidiyon ta na amfani da manhajar InVid mai nazarin hotunan bidiyo, ta gano cewa bidiyon ba sabo ba ne, an fara wallafa bidiyon ne ranar daya ga watan Nuwamban 2019 a shafukan soshiyal mediyan CiTi TV wadanda suka hada da Facebook da YouTube. An wallafa bidiyon da taken „Rufe iyakokin Najeriya: GUTA da GEDA sun bukaci a rufe shagunan baki dan ramako.“
Abu mafi mahimmanci ma shi ne Dubawa ta gano cewa mai zargin ya yi amfani da dakiku 45 ne kacal daga cikin bidiyon wanda ke da tsawon minti 4:23
Ainihin Labarin
Ainihin abun da ya faru a bidiyon ya faru a Ghana ne a shekarar 2019 lokacin da gwamnatin Najeriya ta rufe iyakokinta da makotanta domin hana mutane shigar da kayayyakin masarufi ta barauniyar hanya musamman shinkafa. Sai Kungiyar ‚Yan Kasuwan Ghana (GUTA) da Kungiyar Masu Saida Kayayyakin Lantarki (GEDA) su ma suka yi gangami inda suka bukaci baki su ma su bar mu su nasu kasuwannin dan su rama abin da ake musu.
Wannan taron ne Citi TV tashar yada labaran da ba ruwanta da gwamnati wadda ke da shelkwatarta a Adabraka, Accra Ghana. Kafar yada labaran ta dauki jawabin GEDA da GUDA a matsayin mataki ne na rama rufe iyakokin da Najeriya ta yi domin akwai ‚yan Najeriya da yawa da ke da sana’o’i a Ghana.
Bugu da kari, mutumin da ke jawabi a bidiyon, sunan shi Samuel Addo, kuma shi ne wakilin jama’an GEDA. Labarin dai ya sami yaduwa sosai a shekarar 2019 domin akwai labarin a sauran kafafen yada labarai.
A Karshe
Duk yadda aka yi, wanda ya fara zargin ya nemi ya tayar da zaune tsaye ne domin bidiyon da ma abin da aka yi a cikin bidiyon duk ba a Najeriya ba ne dan haka wannan zargin karya ne.
Discussion about this post