Kotu dake Iyaganku jihar Oyo ta gurfanar da wata mata wacce matsafiya ce mai suna Rasaki Ogunbode mai shekara 51 da wata mata Zainab Bello mai shekara 54 bayan an kama su da laifin yi wa yarinyar mai shekara biyu kaciya ta karfin.
Lauyan da ta shigar da karan Gbemisola Adedeji ta bayyana cewa a ranar 16 da 17 ga watan Disambar 2021 ne Ogunbode da Zainab suka yi wa yarinyar kaciya da karfin tsiya a wani gida dake Sarumi a Asipa dake garin Oyo.
Ta ce yi wa yarinyar kaciya irin haka da suka yi ya saba wa sashe 516 na dokar ‘Criminal Code’ na jihar Oyo ta shekara 2000 da sashe 26 sakin layi 2 na dokar kare hakkin yara kanana na jihar Oyo na shekarar 2016.
Daga nan lauyan dake kare Ogunbode da Zainab, M. O Folorunso ya roki kotu ta bada belin su.
Alkalin kotun S. H Adebisi ya bada belin Ogunbode da Zainab akan Naira 50,000 sannan kowannen su zai gabatar da shaida daya.
Adebisi ya ce za a ci gaba da shari’a ranar 12 ga Maris.
Discussion about this post