Tsohon Shugaban Kwamitin Gyaran Tsarin ‘Yan Fansho na Ƙasa, Abdulrasheed Maina da ke ɗaure a kurkuku, ya na asibiti ya na fuskantar kulawa daga cutar kurumtar da ya kamu da ita, sai kuma matsanancin hawan-jini.
Asibitin Koyarwa na Abuja ne ya tabbatar da haka.
Sannan kuma asibitin ya ce Maina wanda ke fuskantar ɗaurin shekaru takwas, saboda wawurar naira biliyan 2 na kuɗaɗen ‘yan fansho, za a yi masa gwajin ƙwaƙwalwa.
PREMIUM TIMES ta samu kwafen wasiƙar da Asibitin Abuja ya aika wa Babbar Kotun Abuja da ke Jabi, inda Maina ke sake fuskantar wata tuhuma ta wawure naira miliyan 738 na ‘yan fansho.
Wannan tuhumar daban ta ke da wadda aka rigaya aka yanke masa ɗaurin shekaru 8 a kirkuku, a cikin Nuwamba, 2021.
A ranar Talata lokacin zaman shari’a, alƙali Abubakar Kutigi ya yi magana kan wasiƙar da ya ce Asibitin Koyarwa na Abuja ya aiko wa kotun, amma bai karanto ta tiryan-tiryan ba.
Maina dai ba a kai shi kotun daga gidan kurkuku inda ya ke tsare a ranar ba. Sannan kuma lauyoyin sa da lauyan gwamnati mai gabatar da ƙara, babu wanda ya ce ga inda Maina ya ke a ranar.
Halin Rashin Lafiyar Maina:
Wasiƙar da Asibitin Koyarwa na Abuja ya aika wa kotu a ranar 18 Ga Fabrairu, ta faɗo hannun PREMIUM TIMES.
Wani likita ne mai da ya ƙware wajen sanin cututtukan Kunne, Hanci da Maƙogaro (ETN), mai suna I.O Omonua ya sa wa wasiƙar hannu.
“Mai wannan suna a saman wasiƙa ya na samun kulawa daga ɓangaren mu na Kula da Masu Cututtukan Kunne, Hanci da Maƙogaro.
“Ya yi fama da ƙarƙayin maƙogaro, na hanci da na kunne. Sannan kuma ya na kukan yawan toshewar da hancin sa ke yi. Hancin kan riƙa ɗigar da ruwan majina sannan kuma idan ya shaƙi ƙura, turare da wasu sinadarai, ya kan samu matsalar numfashi.” Haka aka rubuta a cikin wasiƙar.
Sannan kuma wasiƙar na ɗauke da bayanin cewa, “Maina ya na fama da lalurar jiwa idan ya kallo ƙasa daga bisa bene ko wani wuri mai nesa da ƙasa.”
Omonuwa ya ce “Maina ya na fama da lalurar kurumta, ba ya ji ta kunnen sa na hagu.”
“Maina ya na fama da ciwon hawan-jini. Duk da ana kula da shi wajen ba shi magani, lamarin ya na da wuyar sha’ani.”
Wasiƙar dai neman amincewar kotu ta ke ƙunshe da shi, domin asibitin ya yi wa Maina gwaje-gwajen kunne, na ƙwaƙwalwa da kuma wasu shirye-shiryen aiki tsakanin 21 zuwa 23 Ga Fabrairu.
“Don haka mu na neman amincewar kotu ta bada damar Asibitin Abuja ya yi wa Maina waɗannan gwaje-gwaje.
Yayin da ɓangaren lauyoyin sa da lauyan EFCC su ka ce ba su samu kwafen wasiƙar ba, a zaman kotu na ranar Talata Mai Shari’a Kutigi ya ɗage sauraren shari’ar zuwa 27 Ga Afrilu, domin kotu ta tuntuɓi Hukumar Kula da Gidajen Kurkuku ta Ƙasa, don sanin inda Maina ya ke.
Waiwaye: Yadda Kotu Ta Yanke Wa Maina Hukunci Cikin Nuwamba, 2021:
Shari’ar Maina: Yadda Bankuna Su Ka Taya Maina Jidar Naira Biliyan 2 Daga Asusun ‘Yan Fansho -Mai Shari’a:
Yayin da ya ke yanke wa tsohon shugaban Hukumar Gyaran. Fansho Abdulrasheed Maina hukunci, Mai Shari’a ya ce bankunan UBA da Fedility Bank sun miƙa wuya Maina ya yi amfani da su wajen satar maƙudan kuɗaɗen da haƙƙin ‘yan fanshon Najeriya ne.
Mai Shari’a ya ce kuɗin da Maina ya sata ya yi sanadiyyar kassara gidajen ɗimbin jama’a tare da talauta masu haƙƙin karɓar fansho.
Dalilin haka ne ya bayyana cewa kamata ya yi a hukunta bankunan tare da Maina, domin su ne su ka karɓi ajiyar kuɗaɗen satar suka ɓoye masa.
“Kamata ya yi a ce an shigar da Bankin UBA da Fedility Bank ƙara a lokaci ɗaya da Maina.”
Abang ya ƙara da cewa “kamata ya yi a ƙwace lasisin UBA da na Fedility.”
“Waɗannan bankuna sun taimaka wa ɓarawon kuɗaɗen gwamnati ya ɓoye kuɗaɗen da ya sata, ya bar ɗimbin masu haƙƙi kan kuɗaɗen cikin baƙin talauci, wasu har ma suka mutu ba su ci moriyar haƙƙin na su ba.
“Shi kuma Maina ya na can sai ɓalle-bushasha ya ke yi, ya na sayen maka-makan gidaje a Dubai da kuɗin da kowa ya san ba daga haƙƙin albashin da ake biyan sa ba ne.”
Maina Ba Shi Da Imani, Ba Shi Da Tausayi -Mai Shari’a:
Da ya ke yanke hukunci, Mai Shari’a ya kira Maina, “mutumin da ba shi da imani, babu tausayi ko kaɗan a zuciyar sa, tunda har ya kwashe sama da Naira biliyan 2 na ‘yan fansho shi kaɗai.
Mai Shari’a ya ce babu ta yadda za a yi Maina ya samu Naira biliyan 2, domin albashin sa na matsayin sa na ma’aikatacin gwamnatin tarayya, kaɗan ya zarce naira 300,000 a duk wata.
“Kai ko da shekaru 35 ya yi ya na tara albashin, ba ya taɓa komai a cikin kuɗin, babu yadda za a yi ya tara naira biliyan 2.1.”
Premium Times Hausa ta kawo labarin yadda kotu ta ɗaure Maina shekaru 8 a kurkuku, bayan an samu sama naira biliyan 2 a hannun sa.
Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta ɗaure Abdulrasheed Maina shekaru takwas a kurkuku, bayan samun sa da laifin wawurar fiye da naira bikiyan biyu daga asusun ‘yan fenshon Najeriya.
Maina wanda Mai Shari’a Okon Abang ya ce ya saci kuɗaɗen a lokacin da ya ke Shugaban Kwamitin Gyaran Tsarin Fansho (PRTT), an kama shi da laifi a tuhumoni masu lamba 2, 6, 9, 3, 7 da 10 da aka yi masa.
Hukumar EFCC ce ta gurfanar da Maina shekaru da dama da suka gabata.
Mai Shari’a ya ce Maina ya saci kuɗaɗen waɗanda ya ce:
“Haƙƙin ‘yan fanshon Najeriya ne, waɗanda yawancin su ma sun mutu ba tare da sun kai ga cin moriyar haƙƙin na su ba.”
Mai Shari’a ya ce ya gamsu da hujjoji da shaidun da masu gabatar da ƙara su ka baje a gaban kotu, waɗanda su ka tabbatar da cewa Maina ya saci maƙudan kuɗaɗen.
“An tabbatar da Maina ya sayi gida kantameme na dala miliyan 1.4 a Abuja.
“Kuma an karya ƙa’ida wajen biyan kuɗin a asirce wuri-na-gugar-wuri, maimakon a biya kuɗin ta banki, kamar yadda doka ta ce duk cinikin da ya haura Naira miliyan 5, to a biya ta banki, ba kuɗi hannu ba.
“An kuma dame shi da kimshe kuɗaɗe a wasu sabbin bankuna biyu, inda ya ɓoye sunan sa, ya ajiye kuɗaɗen da sunan iyalan sa.
“Kuɗaɗen da ya ajiye a bankin sun haɗa da Naira miliyan 300, Naira miliyan 500 da kuma naira biliyan 1.5, waɗanda ya sata daga kuɗaɗen ‘yan fansho.”
Mai Shari’a ya ce Maina ya kasa kare kan sa, sannan kuma gidan da ya saya haƙiƙanin gaskiya ko kusa albashin sa da alawus ɗin sa ko da ya tara su, ba za su iya sayen gidan ba.”
Discussion about this post