• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

    Kano State Assembly

    Dan majalisar dokoki na jihar Kano ya doka ‘Ribas’ bayan ya tsunduma lambun jam’iyyar NNPP, ya ya rungumi tsintsiyar sa ya dawo APC

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

GUGA BA KI TSORON RAMI: Laƙani 20 da Saraki zai rubuce ya shanye 2023 da su

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
February 5, 2022
in Labarai
0
Bukola Saraki prays

Bukola Saraki prays

Idan aka ajiye batun adawa, ko siyasar ɓangaranci da ƙabilanci a gefe, to za a iya cewa Sanata Abubakar Bukola Saraki (ABS) ya dace da shugabancin Najeriya a 2023. Domin idan za a yi zube-ban-ƙwaryar dukkan waɗanda suka nuna sha’awa ko kwaɗayin fitowa takara, babu wanda ya isa ya ture Saraki daga sahun gaba.

A mulki da siyasa dai an fi sanin Saraki gadan-gadan daga lokacin da ya zama Gwamnan Jihar Kwara tsakanin 2003 zuwa 2011.

Bayan kammala wa’adin sa, Saraki ya yi takarar zaɓen fidda gwanin neman fitowa zaɓen shugaban ƙasa a 2011. Sai dai duk da bai samu tikiti ba, ya samu nasarar zama sanata daga Jihar Kwara.

Da guguwar 2015 ta kaɗa, Saraki na a sahun gaban dakka da gaggan waɗanda su ka fice daga PDP, suka koma APC, har ta kai ga Buhari ya yi nasara.

Saraki ya sake nasara kan kujerar sa ta sanata a ƙarƙashin APC. Sai dai a lokacin ne gogan ya nuna wa duniya cewa idan ma ana gadon siyasa, to ya da gaje ta ɗin. Mahaifin sa Olusola Saraki ya yi Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, a zamanin Jamhuriya ta Biyu, wadda aka fi sani da zamanin mulkin Shagari.

Lokacin da aka yi gambizar da ta yi sanadiyyar nasarar Shugaba Muhammadu Buhari a 2015, an ƙulla yarjejeniyar bai wa nPDP muƙamin Shugaban Majalisar Dattawa, kamar yadda aka bai wa ACN muƙamin Mataimakin Shugaban Ƙasa.

Sai dai kuma bayan APC ta yi nasara, an samu akasi a ɓangaren shugaban ƙasa da ‘yan barandan sa, waɗanda suka nemi yi wa Saraki buƙulun zama shugaban majalisar dattawa.

Amma da ya ke Saraki ya san kan-tsiyar siyasa, sai ya nuna shi ai tamkar kurege ne, uban dabarar da ba ya yin rami ƙofa ɗaya.

Fadar Shugaban Ƙasa ba ta ankara ba sai dai ji kawai suka yi har an naɗa Saraki ya zama Shugaban Majalisar Dattawa.

Daga lokacin sai aka riƙa yi faɗan zalɓe da maciji tsakanin Fadar Shugaban Ƙasa da Sanata Saraki.

Zalɓe ne ya haɗiyi maciji dai kan sa. Shi kuma maciji ya kanannaɗe wuyan zalɓe, ta yadda ya kasa haɗiyar miyau ballantana ma ya iya haɗiyar macijin.

Bukola Sarakin Shugaban Majalisar Da Bai San Amshin-Shata Ba:

Shekaru huɗu da Saraki ya yi a shugabancin Majalisar Tarayya, ya ji jiki, amma kuma shi ma ya jigata Fadar Shugaban Ƙasa. Domin a Tarihi ba a taɓa yin Shugaban Majalisar da ya tsone wa Shugaban Ƙasa ido kamar sa ba.

Babu irin tuggu, ‘jamhuru’, kitimirmira da kutunguilar da ba a kitsa wa Saraki ba, don dai a ga bayan sa. Amma ba a yi nasara ba.

Sai da ta kai tun ana bin sa da ƙullin maka shi kotu ya na Shuagaban Majalisar Dattawa, har sai da ta kai ana yi masa barazana da jami’an tsaro. Amma dakakken ya dake, ko gezau.

An kewaye gidan sa, an hana shi fita. An janye masa jami’an tsaro. Kai an, an, an ɗin da aka yi masa su na da yawa. Da mai rarraunar zuciya, da Saraki ya kwanta ƙasa ya yi liƙis, sun bi shi sun ƙarasa.

An bi Saraki da sharri a lokacin, ta yadda duk matsalar da ta faru sai a ce don Saraki na Shuagaban Majalisar Dattawa ne. Sai ga shi bayan ba ya kan kujerar ne ma matsalolin suka fi dabaibaye Najeriya.

Bajekolin Saraki A Zahiri Da Baɗini:

Da dama ba su san baɗinin Saraki ba a lokacin da ya na Gwamnan Jihar Kwara daga 2003 zuwa 2011. Zahirin sa aka fi sani a Majalisar Dattawa.

Bukola Saraki ba ɗan siyasar da za a yi wa gorin rashin iya rigimar siyasa ba ne. Da kowa ma zai iya. Shugaban Muhammadu Buhari da kuma ‘yar’uwar Sarakin Gbemisola Saraki za su iya tabbatar da haka.

Idan batun zaman lumanar siyasa ce, nan ma a sahun gaba ya ke, domin shi ne ma Shugaban Kwamitin Sasanta Hasalallun PDP.

Idan ka ɗaga Saraki a kasuwar hada-hadar darajar ‘yan siyasa, da wahala ka samu wanda zai fi shi farashi ko nauyi.

Tsawon shekaru takwas ɗin da ya yi ya na gwamna a Jihar Kwara, sun isa shaida cewa idan ya samu damar riƙe Najeriya, ba zai yi wasarere da akalar mulki har a koma ana da-na-sanin shiga halin ƙaƙa-ni-ka-yin yaya-za-a-yi ba.

Kaɗan daga abin da al’ummar Jihar Kwara ba za su manta da Saraki ba, shi ne ƙoƙarin sa wajen:

Haɗa garuruwa 375 da tashar wutar lantarki ta ƙasa.

Samar da taransafoma har 735 ga al’ummar garuruwa da yankunan karkara.

Warkar da mutum 45,526 daga cututtukan da suka haddasa masu gani garara-garara ko dundimi.

Yi wa mutum 2,630 aikin warkar da makanta, su ka koma gani Tangaran.

Inganta ilmin firamare da sakandare, ta hanyar samar da wadatar ƙwararrun malamai. Kafin saukar Saraki ta kai yawan malamai za su kai duk ɗalibi ƙasa da 20 na da malami 1. Ba kamar wasu jihohi ba da za ka samu malami 1 da ɗalibai 70 ko fiye da haka.

Saraki ya gina Jami’ar Jihar Kwara a cikin 2009.

Ya inganta matasa ta hanyar gina Cibiyar Bunƙasa Wasan Kwallon Ƙafa ta farko a Najeriya (Kwara Football Academy).

Ya bunƙasa harkokin noma, musamman kafa Shonga Farm, wadda yanzu haka a fannin kiwon kaji ta na cikin manyan gonakin da ake tinƙaho da su a ƙasar nan.

Saraki ya inganta samar da ruwa a dukkan mazaɓu 193 na Jihar Kwara. Ya jina famfon burtsa 1,930 a cikin shekara ɗaya (2006-2007). Wato kowace mazaɓa famfo 10 kenan.

Saraki ya gina rukunin gidaje masu sauƙin kuɗi a wurare 9.

Zamanin mulkin Saraki ne ya gina sabbin Ofisoshin ‘Yan Sanda har guda 25 a cikin Ilorin, babban birnin Jihar Kwara.

Ya bunƙasa hanyoyin samun kuɗin shiga a jihar, daga naira miliyan 64 a duk wata zuwa naira milyan 300 duk wata.

Lokacin da Saraki ya hau mulki cikin 2003, ya gaji bashin naira biliyan 42, amma kafin ya sauka sai da ya biya bashin kakaf.

Ya bayar da bashi har na naira biliyan biyar ga ma’aikatan gwamnati da sauran masu riƙe da muƙamai a Jihar Kwara, domin su sayi hannayen jari a kasuwar hada-hadar hannayen jari.

Tags: AbujaAPCFugaHausaNewsPDPSaraki
Previous Post

APC ta sanar wa INEC ranar da za ta yi gangami Na ƙasa

Next Post

Ba kuɗi Amaechi ya ba ni ba, kishin masarautar Daura da yake da shi ya sa na naɗa shi sarautar Ɗan Amanar Daura – Sarkin Daura

Next Post
Ba kuɗi Amaechi ya ba ni ba, kishin masarautar Daura da yake da shi ya sa na naɗa shi sarautar Ɗan Amanar Daura – Sarkin Daura

Ba kuɗi Amaechi ya ba ni ba, kishin masarautar Daura da yake da shi ya sa na naɗa shi sarautar Ɗan Amanar Daura - Sarkin Daura

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya
  • Gwamnatin Buhari ta ƙakaba sabbin harajin kira na wayar hannu ga ƴan Najeriya
  • BALA’IN ‘YAN BINDIGA: Sama da Katsinawa 13,000 su ka tsallake ba shiri zuwa Jamhuriyyar Nijar -Gwamna Masari
  • TAKARAR SHUGABAN ƘASA 2023: Mutum biyar kaɗai ke da gaske a cikin APC, sauran ‘yan rakiyar amarya ne -Gwamna Fayemi
  • Babu wanda na ke bibiya yayi min mataimakin shugaban kasa – Zulum

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.