• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Yunƙurin Raba Kan Ƴanƴan Ɗarikar Tijjaniyyah, Saboda Hasadar Da Suke Yiwa Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, Daga Imam Murtadha Gusau

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
January 6, 2022
in Ra'ayi
0
Yunƙurin Raba Kan Ƴanƴan Ɗarikar Tijjaniyyah, Saboda Hasadar Da Suke Yiwa Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, Daga Imam Murtadha Gusau

Da Sunan Allah, Mai Rahama, Mai Jinkai

Assalamu Alaikum

Ya ku bayin Allah! Abu ne da kowa ya sani, kuma ya amince, kuma babu wata jayayya akai, cewa hadin kan Musulmi wajibi ne, kuma rabuwa sharri ne, azaba ne kuma bala’i ne. Allah da Manzonsa (SAW) sun umurci Musulmi da su hada kan su. Kuma suka tabbatar masu da cewa, hadin kan nan shine sharadin zaman lafiyar su da ci gaban su. Idan Musulmi sun hada kai, zasu rabauta duniya da lahira. Idan kuwa suka rarrabu, suka ki bin umurnin Allah da Manzonsa, to lallai, tun anan duniya zasu ga mummunan sakamakon aikin su, kafin su tafi lahira, su hadu da Allah mahaliccin su.

Ya ku bayin Allah, wannan hadin kai da Allah da Manzonsa (SAW) suka yi umurni, shine Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje yake kokarin rusawa, da sunan yakar Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, sanadiyyar hasadar da yake nuna masa, kuma wadda taki-ci-taki-cinyewa!

Abu ne da yake a fili karara cewa, tun lokacin da aka nada Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II a matsayin Khalifan Tijjaniyyah a Najeriya, Gwamna Abdullahi Umar Ganduje bai yi kasa a gwiwa ba wurin yakar sa, kamar yadda yake ta yakar sa a can baya, saboda Sarkin ya dage akan cewa, dole ne ayi gaskiya.

Wallahi ba yadda Gwamna Ganduje bai yi ba na ganin cewa ya hana ayi nadin, to amma da yake duk abun da Allah yayi, dan Adam ba ya iya hanawa, sai da Allah Subhanahu wa Ta’ala ya tabbatar da wannan mukami na Khalifanci ga Khalifah Muhammadu Sanusi II.

Bayan da Gwamna Ganduje ya kasa soke nadin Khalifancin, sai ya yanke shawarar cewa bari yabi wata hanyar da duk zai bi, domin dai ya kawowa Sarki Muhammadu Sanusi II matsala. Sanadiyyar haka, sai ya dauki Ibrahim Dahiru Bauchi da Isa Sanusi Bayero (Isa Pilot) domin suyi aiki tare da shi, na ganin ya cimma wannan bakin buri nasa.

Gwaman Ganduje da wadannan mutane, sun yi yunkuri a lokuta daban-daban domin gudanar da zaman Zikiri a masarautar Kano, wanda wai a nasu tunanin, zai zama taron da ba’a taba yin irin sa ba a tarihin masarautar, amma duk basu ci nasara ba. Sai wannan karon kuma basu gajiya ba, suka shirya wani taron na Zikiri, wanda zai kalubalanci taron da aka shirya na duniya a garin Lokoja, domin gudanar da Maulidi tare da yiwa kasa addu’o’in zaman lafiya da samun ci gaba da hadin kai mai dorewa.

Ganduje da mutanen nasa, suna ganin cewa, su a irin nasu fahimtar, idan suka kira wannan taro a Kano, kuma suka sanya shi rana daya da wanda za’a yi a garin Lokoja, to lallai tabbas taron na Lokoja zai hadu da cikas. Kuma idan hakan ya faru, to sun cimma burin su, kuma sun kunyata Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II a idon duniya.

Amma da yake Allah baya zalunci, kuma ya haramtawa kansa zalunci, kuma ya hane mu da yin zalunci, kuma ya tabbatar muna da cewa, tabbas zai ci gaba da kunyata dukkan wani mutum azzalumi a duk inda yake, sai aka wayi gari yunkurin nasu ya hadu da cikas, kuma ya hadu da matsala.

Hakan ya faru ne saboda dukkanin Shehunan darikar Tijjaniyyah na Kano da sauran wurare, sun nuna cewa su fa suna tare da Sarki Muhammadu Sanusi II, kuma sun nuna cewa darikar Tijjaniyyah ba wata haja bace ta sayarwa, bare wani dan siyasa ya saye su da kudi. Sun nuna dattako, kuma sun yanke shawarar kaucewa duk wani abu da ya shafi yunkurin Gwamna Ganduje na zagon kasa ga darikar Tijjaniyyah da Khalifah Muhammadu Sanusi II.

Dukkanin Shehunnai da Khalifofin darikar Tijjaniyyah a Najeriya, sun fahimci abun da yake faruwa na yunkurin raba kawunan su, da kuma tarwatsasu da Gwamna Ganduje yake kokarin yi.

Ya ku bayin Allah! Wallahi wannan matsayi na kafatanin Shehunnan darikar Tijjaniyyah, ya kara jawo masu daraja da matsayi a idon duniya. Domin anyi yunkurin yin amfani da kudi, da kuma karfin gwamnati, amma suka kafe, suka ki yarda, suka zabi su kasance tare da gaskiya, da kuma masu gaskiya.

Kai yanzu ma su Shehunnan darikar Tijjaniyyah, yanzu sun gano wani yunkuri, da wata makarkashiya, na kokarin samar da wata kishiya da zata kalubalanci jagorancin Darikar Tijjaniyyah na duniya baki daya. Shi yasa aka dauki nauyin zuwa kasar Algeria, a dauko Shehunnai can, domin jagorancin da yake a kasar Senegal a yanzu, an kasa sayen su da kudi. Don haka, tun da basu mika wuya ba, to bari a manta da su, ayi hulda da Shehunnan kasar Algeria.

Shi yasa Gwamna Ganduje ya dauki nauyin ziyarar Ibrahim Dahiru Bauchi zuwa kasar Aljeriya akan ya gayyato wani Shugaban Darikar Tijjaniyyah, da sauran Shehunnai da Malamai, domin suzo Kano, domin yin Zikiri a ranar Juma’ah, 7 ga watan Janairun 2022, wai duk domin a dakile wancan muhimmin Zikirin da taron yiwa kasa addu’a, da za’a yi a garin Lokoja, babban birnin jihar Kogi, wato a rana makamanciyarta, wanda gwamnan jihar Kogi, Alhaji Yahaya Adoza Bello, ya roka ayi, kuma ya shirya a garin na Lokaja, kuma taron da Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II ne zai jagorance shi.

Majalisar Shura ta Darikar Tijjaniyyah ta koli ta jihar Kano, kakashin jagorancin Sheikh Abdullahi Uwais Limanci, ta yanke shawarar cewa babu ruwanta da duk wani abu na shirin raba kan al’ummah da Gwamna Ganduje yake son yi.

Idan dai har al’ummar kasar nan zasu iya tunawa, a can baya, Gwamna Ganduje ya bayyana Shehunan Darikar Tijjaniyyah, a matsayin wadanda ba zasu iya tabuka komai ba, domin ceto sarautar Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammdu Sanusi II, a inda yace duk addu’ar da suke yi ba zata yi amfani ba, domin wai “SUN KAMA KAFAR WALA”!

To yanzu dai alhamdulillahi, domin duniya ta yabawa Shehunan Darikar Tijjaniyyah na Kano, da na Najeriya baki daya, saboda sun nuna wa Gwamna Ganduje cewa su ba za’a iya sayen su da kudi ba. Dukkanin su sun yanke shawarar halartar babban taron da za’a yi a garin Lokoja, tare da wakilai daga Kaulaha da kasar Maroko. Kuma alhamdulillahi, galibin mabiya Darikar Tijjaniyyah a Najeriya, sunyi mubaya’ah ga jagorancin Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, a matsayin shugaba daya tilo da Kaulaha da Maroko suka amince da shi.

Kuma alhamdulillahi, yanzu dai ta tabbata cewa, Gwamna Ganduje ya gaza a wurin yakar Darikar Tijjaniyyah, kamar yadda kuma ya gaza a wurin yakar Majalisar Malamai ta jihar Kano, a lokacin da yayi yunkurin tsige Malam Ibrahim Khalil saboda tsananin rashin kunya.

Kamar yadda kuka sani, Gwamna Ganduje da ‘yan kanzagin nasa, sun gayyaci dukkanin Shugabannin Darikar Tijjaniyyah na kasar Senegal, domin su halarci taron na Kano, amma shugabannin sunce sam ba zasu zo ba, domin ba zasu taba bayar da goyon baya akan abun da duk zai raba kan jama’ar su ba.

Ganin cewa Ibrahim Dahiru Bauchi ya kasa shawo kansu, shine sai aka tayar da jirgi na musamman, tare da su Isa Pilot, domin a dauki Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya tafi Senegal, domin a lallashi shugabannin darikar su amince suzo. Amma duk lallashin da aka yi, sun ce sam ba zasu zo Zikirin na Kano ba. To shine, suka samu wasu samari, matasa, daga kasar Senegal din, suka zo da su, domin su halarci taron na Kano, da sunan wai wakilan shugabannin. Idan hakan ya kasance, to wai su a ganin su, basu kunyata ba!

A can baya idan kun tuna, Gwamna Ganduje yayi amfani da wasu bara-gurbi, marasa kishi, ya samu nasarar ruguza Masarautar Kano mai tarin albarka, mai dimbin tarihi, mai cike da kima da kwarjini, wanda a halin yanzu ya mayar da Masarautar wani dandali na shiririta, ta hanyar zalunci.

Da ikon Allah, muna nan muna ta addu’a da rokon Allah, da fatan Allah ya kawo wa Kanawa da jihar Kano adalin Gwamna, wanda zai dawowa da jihar Kano, da kuma Masarautar Kano da kwarjinin nan nasu da Allah ya basu, kuma da ikon Allah, ya gyara dukkanin barnar da Gwamna Ganduje yayiwa jihar!

Sannan ina mai tabbatar maku da cewa, Gwamna Ganduje da duk ‘yan kanzagin nasa, ba zasu taba cin nasara a dukkan wani mummunan tanadi, da wani yunkurin sharri nasu ba. Kuma zasu ci gaba da takaicin abin da ya shafi Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II; domin shi Sarki Muhammadu Sanusi II wallahi yin Allah ne, ba yin kansa bane. Kuma liyafah da karramawa da aka yi masa kwanan nan a kasar Ghana, shaida ce dake nuna matsayinsa da daukakar darajarsa.

Kuma a daya gefen, ya kamata Gwamna Ganduje ya san da cewa, ikonsa da mulkinsa ba zasu iya tsallakawa zuwa ko’ina a Najeriya a fadin Najeriya ba, idan ba Kano kawai ba. Amma ikon Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, wanda yake yiwa hassada, wallahi ya wuce nahiyar Afirka, ya shiga duniya ko’ina. Wannan kuwa daga Allah ne.

Daga karshe, muna sanar da jama’ah cewa, bayan taron Zikiri da yiwa kasa addu’a, da aka saba gabatarwa a Masarautar Kano tare da Shehunnan darikar Tijjaniyyah, wato wanda ake gabatarwa a watan Muharram sau daya a shekara, bamu san da wani taron Zikirin da wasu suka shirya domin raba kan jama’ah ba. Muna kira, da ku kauracewa duk wata sanarwar gayyatar Zikiri da ake yadawa, wai za’a yi a Kano. Duk wani taro da bai sami izinin Khalifofin Shehu ba, kada su halarce shi. Dukkanin Shehunnai ba zasu halarta ba. Taron Lokoja shine halattacen taro. Idan kana da iko can zaka je. Idan kuwa babu halin zuwa, to ana kira ga ‘yan uwa da su zauna a zawiyoyinsu suyi Zikiri.

Kuma mun samu tabbataccen labari cewa an dauki nauyin ‘yan jagaliya, da wasu ‘yan kungiyoyi, da zauna-gari-banza, za’a biya su makudan kudade, domin su halarci taron da aka shirya a Kano din domin raba kan jama’ah. Wai da nufin su nunawa duniya cewa, sun shirya taron Zikiri, kuma an amsa kira. Don haka jama’ah, ayi hankali!

Alhamdulillah, a yau din nan, kuma a yanzun nan, da karfe biyar daidai (5:00 pm) na yammacin ranar alhamis, 06/01/2022, da nike wannan rubutu, domin sanar da duniya hakikanin halin da ake ciki, domin kar su yarda a rude su karyar banza, Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, shi da tawagarsa, da sauran Khalifofi, da Shehunnai da mukadamai, kai da duk wani mai fada aji a cikin Darikar Tijjaniyyah, a Najeriya da kewaye, duk sun sauka, sun halara a garin Lokoja.

Kuma yanzu ana tsakiyar cigaba da shirye-shiryen gabatar da Maulidi da Zikiri da yiwa kasa addu’a da rokon Allah na musamman, a garin na Lokoja, jihar Kogi.

Sannan ya ku bayin Allah! Ya ku masoya Mai Martaba Sarkin Kano Khalifah Malam Muhammadu Sanusi II, ku sani, wallahi lokaci yayi da ya kamata mu nuna kishin mu tsantsa akan Khalifah Muhammadu Sanusi II. Ku sani, duk wannan kiyayyar da ake nunawa Khalifah Muhammadu Sanusi II ba komai bane illa tsantsar hassada, kiyayya da gaba. Hakan kuma bai samu ba sai da hadin kan Gwamnati, da kuma wasu bara-gurbi. Don haka, ya kamata soyayyar mu ta zama a zahirance, a aikace, zuwa ga Khalifah, ba wai a hoto kawai, ko a baki ba. Ya zama dole, kuma tilas, mu nuna, ta kowane hali, cewa, muna tare da Mai Martaba Khalifah Muhammadu Sanusi II.

Ina addu’a da rokon Allah ya karawa Khalifah lafiya, imani da nisan kwana; kuma Allah yasa ya ga bayan dukkanin makiyansa, amin.

Wassalamu alaikum,

Dan uwan ku: Imam Murtadha Muhammad Gusau ne ya rubuta, daga Okene, Jihar Kogi, Najeriya. Za’a iya samun sa ta lambar waya kamar haka: 08038289761.

Tags: AbujaNewsPREMIUM TIMESSanusiSarkiTijjaniyyah
Previous Post

‘Rudu da hauragiyar ‘yan siyasa ne kawai wai zan koma APC, amma kuma fa bari muga yadda gaba zata kasance’ – Kwankwaso

Next Post

‘Yan bindiga sun yi garkuwa da ‘yan Chana uku, sun kashe masu gadin su biyu a jihar Neja

Next Post
BIDIYON HARBO JIRGI: Shirgegen Karya Boko Haram su ke yi – In ji Rundunar Sojin saman Najeriya

'Yan bindiga sun yi garkuwa da 'yan Chana uku, sun kashe masu gadin su biyu a jihar Neja

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • KATSINA BA DAƊI: Mahara sun buɗe wa tawagar Buhari wuta a yankin da su ka bingige Kwamandan ‘Yan Sandan Dutsinma
  • Takardun sakandare na sun yi layar-zana, amma ina da sakamako mafi kyau -Okowa, mataimakin takarar Atiku
  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.