A ranar 14 Ga Janairu ne wani gungun dakkan ‘yan bindiga suka shiga garin Ɗankade da ke ƙarƙashin Ƙaramar Hukumar Wasagu, su ka kashe mutum 17 sannan suka tasa ƙeyar wasu da dama zuwa cikin daji.
Wannan farmaki da aka kai masu, maharan sun yi ne dma matsayin hukunci, saboda sun karya dokar da su ‘yan bindigar su ka gindaya wa mutanen garin da sauran wasu garuruwa huɗu da ke wajen.
Mutanen Ɗankado a Wasagu sun ƙi biyan ‘yan bindiga harajin-jiki-magayi, har na naira milyan 25. Haka dai waɗansu ‘yan garin da suka tsira da kyar suka shaida wa PREMIUM TIMES Hausa.
‘Kebbi Ba Lafiya: Tsawon Shekaru Uku Kenan ‘Yan Bindiga Ke Mulkin Mu’:
Mazauna yankin sun shaida wa PREMIUM TIMES cewa tsawon shekaru uku ‘yan ta”adda ne ke mulkin yankunan na su, sai yadda suka ga dama su ke yi.
“Yaran Bello Turji ne, kuma daga Akao su ke gudanar da mulkin su. Akao wani ƙauye ne da ke kan iyakar Kebbi da Zamfara.”
Lokacin da su ka kai harin kwanan nan, sun riƙa harbi su na banka wa gonaki da gidaje wuta har tsawon sa’o’i mssu yawa.
Kebbi Ba Lafiya: ‘Ku Biya Naira Miliyan 25, Ko Ku Baƙunci Lahira’ -Inji ‘Yan Bindiga:
Waɗannan ‘yan bindiga dai sun ƙaƙaba harajin-jiki-magayi kan mutanen Ɗankade, wanda tilas suka riƙa biya ta hannun Dagacin garin. Haka majiya ta shaida wa PREMIUM TIMES.
Mazauna ƙauyen kan tara wa ‘yan bindiga miliyoyin nairori duk wata a matsayin haraji, kuma tun farkon 2020 su ke yin haka.
Cikin Disamba 2021 sai ‘yan bindiga suka ƙara farashin harajin da suke karɓa, zuwa Naira miliyan 5 kan kowane ƙauye da suka haɗa da ƙauyukan Klango, K’Daba, Kurgiya, Ragaam da Ɗankade. Suka ce lallai tilas kafin Disamba ya ƙare kowane Dagaci ya tabbatar ya karɓo harajin yankin su ya kai masu.
Wulaƙancin ‘Yan Bindiga A Kebbi: ‘Ku Riƙa Biyan Harajin Naira Miliyan 5, Kuma Ku Riƙa Ba Mu Matan Ku Da ‘Yan Mata Mu Na Kwana Da Su’ -Inji ‘Yan Bindiga:
“Banda harajin tilas na Naira miliyan 5, ‘yan bindiga sun nemi a riƙa ba su matan aure masu jini a jika da ‘yan mata su na kwana da su.”
Wani mai rajin kare haƙƙin jama’a ne mai suna Bamaiye Aniko ya shaida wa PREMIUM TIMES haka.
An kai wa mutanen yankin wannan mummunan hari ne saboda sun ƙi yarda su riƙa miƙa masu matayen su da ‘yan mata ta ‘yan bindiga su na kwana da su.
PREMIUM TIMES ta samu hotunan yadda aka banka wa gidaje da gonaki wuta, sai kuma hotonan wasu da aka ƙona da waɗanda aka harbe.
Baya ga waɗanda aka harbe da waɗanda aka ƙone, an arce da mutane da dama.
“Hatta wasu da aka arce da su ɗin ma an kashe su ta hanyar ƙone su ƙurmus. Ko gawarwakin su ma ba a bari ‘yan uwan su sun bizne ba.” Inji Aniko da ya ke wa PREMIUM TIMES ƙarin bayani.
Yayin da mutanen yankin su ka tabbatar an kashe kimanin 50, rundunar ‘yan sandan jihar ta ce adadin bai kai haka ba. Sannan kuma an kashe sojoji biyu da ɗan sanda ɗaya. Kakakin ‘Yan Sandan Kebbi Nafi’u Abubakar ya tabbatar da kisan sojojin da ɗan sandan a Ɗankade.
Wani mai suna Ibrahim ya shaida wa wakilin PREMIUM TIMES cewa ya rasa iyalin sa gaba ɗaya, an kashe su kuma an ƙone masa gida da dukiya.
Kwanaki huɗu bayan kisan-gilla da banka wa gonaki da gidaje wuta a Ɗankado, wannan jarida ta tabbatar da cewa an yi garkuwa da mutum 29 a ƙauyen Ayu, Waɗanda ko rahoton kama su ba a kai gaba ba.
PREMIUM TIMES ta na da jerin sunayen waɗanda aka kama da waɗanda aka kashe.
A cikin 2021 kaɗai ‘yan bindiga sun kashe sama da mutum 200 a jihar Kebbi. Binciken PREMIUM TIMES ne ya tabbatar da haka.
Discussion about this post