Yayin da aka fara zaman Majalisar Tarayya na sabuwar shekarar 2021 cikin watan Fabrairu a lokacin, babban abin da kowane ɗan Najeriya mai gaganiyar neman yadda zai ciyar kan sa ya riƙa tunani, shi ne yadda Mambobin Majalisar Tarayya za su fito da dokokin gaggawa domin gwamnati ta gaggauta rage wa jama’a raɗaɗin ƙuncin rayuwa sanadiyyar ɓarkewar cutar korona.
To amma idan ka ɗebe batun kasafin kuɗi da kuma yawan amince wa Shugaba Muhammadu Buhari ya ciwo bashi, babu wani tasirin kirki da su ka yi domin rage wa jama’a zafin ƙuncin rayuwar dalilin annobar korona.
Abin takaici, sai Majalisar Tarayya da gwamnatin tarayya su ka fara cacar-baki’ a kan ma’aikata 774,000 da za a ɗauka domin yi wa gwamnati aikin leburancin, shirin da Ma’aikatar Ƙwadago za ta kula a ƙarƙashin ta.
Haka nan kuma sai ‘yajalisa su ka kasa tambayar kan hanzarin Buhari na neman amincewa ya riƙa biyan mutum miliyan 40 Naira 5,000 da ya ce zai riƙa yi idan an cire tallafin fetur.
A taƙaice dai an samu ci gaba da tasiri cikin Majalisar Tarayya a 2021, kuma an sha fama da takidin ‘yan gangan da kuma tuggun ‘yan gargar.
Majalisar Tarayya A 2021: Tasirin ‘Yan Gaske:
Cikin shekarar 2021 ne Majalisar Tarayya ta karya ƙofi da makarun da aka yi wa Ƙudirin Gyaran Dokar Man Fetur, wanda ya shafe shekaru 17 a majalisar tarayya ana ina-ni-ka-ina-ni-ka-aje da shi. Yanzu dai Shugaba Muhammadu Buhari tuni ya sa wa ƙudirin hannu ya zama doka.
Abu na biyu kuma shi ne Ƙudirin Dokar Canjin Yanayi wanda Majalisa ta miƙa, shi ma Buhari ya sa masa hannu a cikin 2021 ya zama doka.
Ƙudirin wanda Honorabul Samuel Onigbo ya gabatar, ya sha fama da jijjige-jijjige, kauce-kauce da kakkaɓe-kakkaɓe a baya.
Sasanta Tankiya Da Saɓani A Gwamnati:
Majalisar Tarayya ta yi abin ƙwarai wajen sasanta rashin jituwa tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyi.
Ta sasanta Gwamnatin Tarayya Ƙungiyar Malaman Jami’o’i (ASUU), wanda Kakakin Majalisar Tarayya Femi Gbajabiamila ya jagoranta.
Haka cikin Disamba Gbajabiamila ya shugabanci zaman sasanci tsakanin Najeriya da UAE domin ɗinke ɓarakar da ta tashi kan jigilar fasinjoji tsakanin ƙasashen biyu.
Gano Kuɗaɗen Da Ma’aikatu Suka Karkatas:
Cikin 2021, Majalisar Tarayya ta yi aƙalla zama 10 da Ministar Kuɗaɗe Zainab Ahmed, Ministan Shari’a Abubakar Malami, Akanta Janar na Tarayya Mai Binciken Kuɗaɗe, Shuagan EFCC Abdulrashid Bawa da wasu shugabannin hukumomi.
Majalisa ta gano yadda Ma’aikatun Gwamnatin Tarayya da Cibiyoyin Gwamnantin Tarayya da Hukumomi ba su maida kuɗaɗen da su ka rage a ƙarshen shekara, tsawon shekaru da dama.
Wasu ma’aikatun ma har yanzu ba su bin tsarin ajiyar kuɗaɗen gwamnati a Asusun Bai-ɗaya (TSA).
Majalisa ta gano kuma ta riƙa kafa kwamitin bincike. Sai dai har yanzu kwamiti bai kammala ba, tsawon watanni shida kenan, saboda yanzu bincike ya koma cikin bankunan da ake kimshe kuɗaɗen.
Majalisar Tarayya A 2021: Takidin ‘Yan Gangan Da Tuggun ‘Yan Gargar:
Lokacin da aka yi hayaniyar rufe shafin Tiwita dai Majalisar Tarayya na hutu. Wasu mambobin musamman ‘yan adawa sun riƙa kartar ƙasa su na cewa idan su ka koma majalisa da ga hutu, za su tada ƙayar baya, sai gwamnatin tarayya ta buɗe Tiwita.
Ana komawa sai Kakakin Majalisar Tarayya Gbajabiamila ya shiga, ya fita ya yi biji-biji da batun. A ƙarshe dai ya kafa kwamitin bincike. Kwamiti kuma ya goyi bayan kulle Tiwita.
Majalisar Tarayya A 2021: Yawan Mutuwar ‘Yan Majalisa Laifin Masu Damun Su Da Maula Ne -Ben Kalu
Shekarar 2021 ta ci rayukan wasu ‘Yan Majalisar Tarayya. Mutuwa ta ɗauki ran Ossy Prestige, inda ta bi shi har cikin asibitin ƙasar Jamus ta ɗauki ran sa a ranar 9 Ga Fabrairu, 2021.
Cikin watan Maris kuwa rayukan ‘yan majalisa biyu mutuwa ta ɗauka. Akwai Haruna Maitala, wanda ya rasa ran sa sakamakon hatsarin mota, tsakanin Keffi zuwa Abuja, kan hanyar sa ta komawa Abuja daga Jos. Sai Hassan Kila wanda ya rasu a Babban Asibitin Tarayya na Abuja.
Cikin watan Afrilu Adebayo Omolefe ya rasu a Asibitin Gwamnonin Tarayya (FMC) da ke Owo, Jihar Ondo.
Sai da kuma Kakakin Yaɗa Labaran Majalisar Tarayya, Ben Kalu, ɗan APC daga Jihar Abia, ya danganta mutuwar ta su da yawan damun su da ake yi da bani-bani, roƙon kuɗi da maula, musamman daga jama’ar mazaɓun su.
Majalisar Tarayya A 2021: Yunƙurin Ƙaƙaba Wa Jaridu Takunkumi Bai Yi Nasara Ba:
Haka kawai wani Segun Odebunmi, ɗan APC daga Jihar Oyo, wanda ko ‘bihim’ bai sani ba a aikin jarida, ya bijiro da ƙudirori biyu domin kafa wa jaridu da soshiyal midiya takunkumi.
Jaridu da Ƙungiyoyin Kare Marasa Karfi kuwa su ka riƙa ragargazar yunƙurin na su, har dai a ƙarshe tilas aka janye ƙudirorin biyu, ɗaya na NBC ɗaya kuma na NPC.
Cikin 2021 an sha gwagwarmaya da Ƙudirin Dokar Fetur, to kuma an ga yadda a ƙarshe aka yi wurgi da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe.
Shin ko ya Majalisar Tarayya za ta kasance a 2022? Muna jira, muna ji, muna gani, muna kuma saurare.
Discussion about this post