Hukumar NCDC ta bayyana cewa cutar kwalera ta yi ajalin mutum 3,604 a shekarar 2021 a Najeriya.
Alkaluman yaduwar cutar na mako 52 da hukumar ta fitar ya nuna cewa shekarar 2021 itace shekarar da cutar ta fi yaduwa da kisan mutane a kasar nan.
Hakan ya faru ne saboda yadda gwamnati ta fi mai da hankali ta wajen yaki da cutar korona.
A shekarar 2021 mutum 111,662 ne ake zaton sun kamu da cutar a kasar nan.
Yaduwar cutar
A shekarar 2021 cutar ta bayyana a kananan hukumomi 435 a jihohi 33 a Najeriya.
Hukumar ta ce yankin Arewa ce yankin da ta fi fama da yaduwar cutar a shekarar 2021.
Jihohin Bauchi mutum 19,558, Jigawa mutum 15,141 da Zamfara mutum 11,931 na daga cikin jihohin da suka fi fama da yaduwar cutar a Arewacin Najeriya.
Abubuwa 10 dake haddasa barkewar cutar a kasar nan
1. Rashin tsafta da barin ƙazanta a gida, musamman abinci da kayan abinci ko kwanukan cin abinci.
2. Zubar da tulin shara da bola aikin unguwanni, wadda ruwan sama ke maida ƙazantar ta s cikin jama’a.
3. Zubar da shara ko bola ko bayan gida a cikin ƙaramu da magudanan ruwa.
4. Yin bayan gida a fili ko a kan bola.
5. Rashin ruwa mai tsafta a cikin al’umma.
6. Ƙarancin asibitocin kula da marasa lafiya a cikin jama’a marasa galihu.
7. Ƙaranci ko rashin magungunan da za a bai wa mai cutar kwalara cikin gaggawa.
8. Matsalar ƙarancin jami’an kiwon lafiya a cikin jama’a.
9. Rashin hanyoyi masu kyau da za a garzaya asibiti da mai cutar amai da gudawa cikin gaggawa.
10. Shan ruwan ƙarama ko kogi, wanda ake zubar da shara, kashin dabbobi da kuma bayan gida.
Discussion about this post