• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    RUƊANI A APC: Gwamnan Neja, Bello ya ɗare kujerar Buni, Buhari ya bada umarnin Buni ya sauka daga shugabancin jam’iyyar

    IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    Barayi sun lalata tiransifoma 20 cikin makonni uku – Kamfanin Raba Wutar Lantarki

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    SADAKA GUZURIN KIYAMA: Tsohon gwamnan da ya taya akanta jidar naira biliyan 84, ya yi wa malamai da ‘yan APC watandar shanu 370, ragunan layya 3,500 a Zamfara

    ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: INEC za ta raba kayan aiki marasa hatsari daga Owerri

    ZAƁEN GWAMNAN OSUN: Matsalar tsaro da guguwar sayen ƙuri’u ne abin da ya fi damun mu -INEC

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    Ƴan sanda sun ceto ƙananan yara 50 da aka kulle cikin kurkukun wani coci a ƙarƙashin ƙasa, a Ondo

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    ‘Na sadaukar da rayuwa ta ga Najeriya’ – Inji sojan da mahara su ka kashe a harin Shiroro

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su kai wa sojoji da mobal farmaki

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    JIHAR NEJA TA KAMA WUTA: Mahara sun kashe sojoji 30, mobal 7, farar hula da dama

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

    HARIN JIRGIN KASA: Ɗaya daga cikin waɗanda ƴan bindiga suka saki ta yi zanga-zanga a Kaduna

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    LMC ta ci tarar Kano Pillars, ta kori shugabanta, Jambul bayan ya gobza wa ‘Rafiri’ naushi a haɓa

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    Inganta Rayuwar Matasa Ta Hanyar Wasan Kwallon Kafa Da Gudunmawar Al’Ummah A Jigawa, Ahmed Ilallah

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

ISKA NA WAHALAR DA MAI KAYAN KARA: Nnamdi Kanu ya kai ƙarar Buhari ga jakadun Amurka da na Birtaniya

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 13, 2022
in Labarai
0
Nnamdi-Kanu

Nnamdi-Kanu

Shugaban Ƙungiyar ‘Yan Taratsin IPOB Nnamdi Kanu, ya rubuta wa Jakadar Amurka a Najeriya, Mary Beth Leonard wasiƙa, mai ɗauke da ƙorafin neman ta tura wakili domin ya zauna ya kalli zaman shari’ar sa da ake yi a Babbar Kotun Tarayya, Abuja.

Kanu na fuskantar tuhuma a gaban Mai Shari’a Binta Nyako ta Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja.

Haka kuma ya rubuta ya rubuta irin wannan wasiƙa ga Jakadan Birtaniya a Najeriya, Catriona Laing, ita ma ya na roƙon ta aika wakilai domin su kalli shari’ar sa a mako mai zuwa.

Za a ci gaba da tuhumar cin amanar ƙasa da zargin ta’addancin da ake yi wa Kanu a ranar 18 Ga Janairu.

Har yanzu dai ya na tsare a Hedikwatar DSS tun cikin watan Yuni, 2021, bayan kamo shi da aka yi daga ƙasar Kenya. Wannan kamowa ce lauyoyin sa ke cewa “garkuwa” ce aka yi da shi.

Lauyan Kanu mai suna Ifeanyi Ejiofor ne ya rubuta wa Amurka da Birtaniya wasiƙar a ranar 11 Ga Janairu.

Takardar dai ta nemi a yi wa Kanu adalci a tuhuma da shari’ar da ke yi da shi.

Lauyan ya ce akwai siyasa a cikin shari’ar Kanu, shi ya sa su ke buƙatar Amurka da Birtaniya su sa-ido a shari’ar.

Cikin wasiƙar, lauyan ya nuna damuwa kan kalaman Shugaba Muhammadu Buhari kan Kanu, inda a hirar da NTA ta yi da shi ya bayyana dalilin da ya sa ba zai tsoma baki a saki Kanu ba.

A hirar dai Buhari ya ce an bai wa Kanu damar kare kan sa, maimakon ya riƙa surfa wa Najeriya zagi daga waje.

“Ba zai yiwu ya koma daga wata ƙasa ka na aikata ayyukan cin amanar ƙasa ba, sannan an kamo ka, ka ce ba za ka girbi abin da ka shuka ba.” Inji Buhari a cikin tattaunawar.

Dalilin Ba Ya Ba Ba Zan Tsoma Baki A Saki Nnamdi Kanu Ba -Buhari:

Shugaba Muhammadu Buhari ya bayyana cewa ba zai tsoma baki ya ce a saki Nnamdi Kanu ba, saboda yin hakan katsalandan ne a cikin fannin shari’a.

Haka Buhari ya furta a wata tattaunawa da aka yi da shi a Gidan Talabijin na Channels, wadda aka nuna a ranar Laraba da dare.

“Akwai hukuma ɗaya wadda ba zan taɓa yi mata katsalandan ba. Ita ce ɓangaren shari’a.” Inji Buhari.

“Mun ba shi damar da zai kare kan sa a Najeriya, maimakon ya riƙa surfa mana zagi daga Turai.”

Da ya ke magana, Buhari ya ce ba za a saki Nnamdi Kanu ba, sai dai ya kare kan sa a kotu kawai.

“Masu cewa a saki Nnamdi Kanu, to ba za a sake shi ba, saboda ba zai yiwu ka riƙa aika saƙonnin da ba gaskiya ba ne a kan tattalin arzikin ƙasa da tsaron ƙasa, sannan kuma ka ce wai ba za ka girbi abin da ka shuka ba.”

Shari’ar Kanu Da Ziyarar Dattawan Igbo Fadar Shugaban Ƙasa:

Watanni biyu da suka gabata ne wannan jarida ta buga labarin yadda dattawan ƙabilar Igbo su ka faɗi ba nauyi, su ka tashi ba nauyi a gaban Buhari, yayin ziyarar neman a saki Kanu da suka kai Fadar Shugaban Ƙasa.

Shugaba Muhammadu Buhari ya shaida wa wasu dattawan ƙabilar Igbo cewa ba zai shiga hurumin ɓangaren shari’a ba, domin ya saki Nnamdi Kanu, wanda a yanzu batun tuhumar da ake masa na kotu.

Buhari ya yi wannan furucin ne yayin wa wasu gungun manyan dattawan ƙabilar Igbo su ka kai masa ziyarar roƙon ya saki Nnamdi Kanu da ke tsare.

Nnamdi Kanu, wanda shi ne Shugaban Ƙungiyar IPOB masu rajin ɓallewa daga Najeriya ko da tsiya, ya shiga hannun hukuma ne yayin da aka kamo shi daga waje, bayan ya tsallake ƙasar nan daga belin sa da aka bayar.

Shugaban tawagar mai suna Mbazulike Amaechi, ya shaida wa Buhari cewa sun zo ne domin su roƙe shi alfarmar ya saki Nnamdi Kanu domin a samu zaman lafiya a yankin Kudu maso Gabas.

Mbazulike, wanda dattijo ne mai shekaru 93 a duniya, ya shaida wa Buhari cewa a cikin ministocin da aka yi a Jamhuriya ta ɗaya, shi kaɗai ne ya rage a duniya.

“Ina roƙon Shugaban Ƙasa ya yi alfarmar cewa idan ya saki Kanu, ni da kai na zan sa masa takunkumin hana shi yin irin kalaman ɓatuncin da ya ke yi.

“Na kasance dattijon da ake girmamawa a Yankin Kudu maso Gabas sosai. Ina roƙon a ba ni shi domin dama ce ta samar da zaman lafiya a yankin mu.

“Ya mai girma Shugaban Ƙasa, yankin mu ya shiga cikin gagarimar matsala saboda tashe-tashen hankulan da ake yi dalilin IPOB.

“Harkokin tattalin arziki sai ja baya su ke yi. Ga kuma harkar ilmi ta shiga garari. Matsalar tsaro kuma sai ƙara ƙamari ta ke yi.

“Na yi amanna da cewa a bi matakin diflomasiyyar siyasar cikin gida a wanzar da zaman lafiya a yankin shi ne mafi alheri, ba amfani da ƙarfin soja ba.

“Ba zan yi fatan na mutu na bar yankin mu cikin tashin hankalin da ya ke ciki ba a yanzu.

“Shugaban Ƙasa wannan dama ce gare ka cewa idan ka saki Kanu, ka zama shugaban da ya samu yankin mu ciki rikici, amma ya wanzar da zaman lafiya a yankin.”

Jawabin Buhari Ga Dattawan Ƙabilar Igbo Masu Roƙon Ya Saki Nnamdi Kanu:

Buhari ya shaida wa Mbazulike cewa ba zai so ya shiga hurumin ɓangarorin gwamnati ba, domin fannin Shari’a ba ɓangaren sa ba ne.

“Na tabbata babu wanda zai iya fitowa ya ce a tsawon shekaru shida da na yi a kan mulki, na yi wa ɓangaren Shari’a katsalandan ko sau ɗaya.

“Da farko dai ina jinjina maka a matsayin ka na dattijo wanda ya haura shekaru 90, amma kaifin tunanin ka garau ya ke. A yanzu haka akwai masu rabin shekarun ka a duniya, amma idan su na magana, ba su iya kama-tasha.

“Kuma ina yi maka ta’aziyyar mutuwar matar ka, wadda ta bar duniya kwanan nan.

Batun Kanu kuwa abu ne mai matuƙar wahalar da zan sa baki a kai. Amma zan duba na ga mai iya yiwuwa.

“Lokacin da ya tsare daga belin da aka bayar na shi, da aka kamo shi aka dawo da shi. Ai gata mu ka yi masa da muka ce idan
ya na da wata jayayya, ya tafi kotu.”

Mbazulike ya sha wa Buhari alwashin cewa sakin Nnamdi zai samar da zaman lafiya a yankin Kudu maso Gabas.

“Ni ba ni goyon bayan IPOB, ina ƙaunar kasancewar Najeriya dunƙulalliyar ƙasa ɗaya.”

Tawagar dai ta mutum shida ce, ciki kuwa har da Chukwumeka Ezeife.

Tags: HausaLabaraiNnamdi KanuPREMIUM TIMES
Previous Post

MAJALISAR DATTAWA: Sai mun sauka Ƴan Najeriya za su riƙa yaba ayyukan alherin mu – Sanata Lawan

Next Post

Gwamnatin Buhari ta sakar wa masu amfani da Tiwita mara, amma ta gindiya sharuɗɗa

Next Post
Lalacin gwamnatin Buhari ya sa Tiwita ya bude ofishinsa na Afirka a kasar Ghana ba Najeriya ba – PDP

Gwamnatin Buhari ta sakar wa masu amfani da Tiwita mara, amma ta gindiya sharuɗɗa

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Takardun sakandare na sun yi layar-zana, amma ina da sakamako mafi kyau -Okowa, mataimakin takarar Atiku
  • HAJJIN BANA: Hankulan maniyyatan Kano 1,238 ya tashi saboda kasa kwashe su kan lokacin rufe filin jirgi Jeddah
  • IHU BAYAN HARIN SHIRORO: Gwamnatin Neja ta dakatar da haƙar ma’adinai a Shiroro, Munya da Rafi
  • 2023: Ka zaɓi El-Rufai mataimaki, ‘ka yi nasara a zaɓe kamar yankan wuka’ – Kira ga Tinubu
  • RIKICIN PDP: Kwamitin Amintattun PDP ya tura wa Wike tawagar lallashi

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.