Gwamnonin da aka zaɓa a ƙarƙashin jam’iyyar PDP sun yi kakkausan kira ga Majalisar Dattawa da ta Tarayya cewa su sa ƙafar da dokar Najeriya ta ba su izni, su take hukuncin da Shugaba Buhari ya ɗauka na ƙin sa wa Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe hannu, su sa masa hannun kawai.
Gwamnonin sun cimma wannan matsaya ce kuma suka bayyana wa manema labarai, a cikin takardar bayanan bayan taron da su ka karanta wa ‘yan jarida, bayan kammala taron su ranar Litinin a Fatakwal, babban birnin Jihar Ribas.
Sun ce babu wani zaɓin da ya rage wa ‘yan majalisa dattawan su da wakilan su, sai kawai su danƙara wa dokar hannu, su yi wa matakin da Buhari ya ɗauka abin nan da ake kira ‘sawun-giwa-take-na-raƙumi.’
A ranar Talata ɗin nan ce Majalisa ke komawa aiki, bayan hutun Kirsimeti da na Sabuwar Shekara da suka tafi. Kuma an haƙƙaƙe cewa batun ƙudirin ne zai tada ƙura sosai idan majalisun biyu sun zauna.
Su kuma gwamnonin PDP sun yi kira ga Majalisa “ta yi watsi da dalilan Buhari na ƙin sa wa dokar hannu, su sai su saka mata.”
Sun ce hakan zai zama “gargaɗi ga Buhari cewa kada ya sake irin wannan hukuncin-gabagaɗi. Domin bai kamata shugaban ƙasa ya sa ƙafa ya murtsuke matakan gyaran tsarin dimokraɗiyya ba.”
Gwamna Aminu Tambuwal na Jihar Sokoto, wanda kuma shi ne Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin PDP ya karanta wa manema labarai takarar bayan taron, wadda ke ƙunshe da wannan buƙata ta su.
Sannan kuma gwamnonin PDP sun ɗora laifin ƙara taɓarɓarewar tsaro a kan Gwamnatin Tarayya, domin ta ƙi amincewa kowace jiha ta kafa ‘yan sandan kan ta, domin shawo kan ta’addanci da hare-haren ‘yan bindiga.
“Taron na mu ya nuna matuƙar damuwa ganin yadda Shuagan Ƙasa ke maida hannun agogo baya, kan harkar tsaro da kuma gyaran dokar zaɓe.”
Sun ce kafa ‘yan sandan jiha abu ne mai muhimmanci ga daƙile ‘yan bindiga, haka gyaran dokar zaɓe na da muhimmanci ga dimokraɗiyya.
Sai dai Buhari ya ce idan aka kafa ‘yan sandan jiha, za su zama ‘yan amshin Shatan gwamnoni.
Gwamnoni 10 ne daga cikin 13 na PDP su ka halarci taron, wanda Gwamna Nysom Wike na Ribas ya zama mai masaukin baƙi.
Maida Hannun Agogo Baya: Yadda Buhari Ya Aika Wa Majalisar Dattawa Wasiƙar Fatali Da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe:
Shugaba Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya wasiƙar sanar da su cewa bai yarda da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe na 2021 ba, don haka ba zai sa wa dokar hannu ba.
Fatali da ƙudirin na ciki wasiƙar da Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya a ranar Talata ɗin nan, kuma majalisun biyu duk su ka karanta wasiƙun na shi a zaman ranar Talata ɗin nan.
Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ne su ka karanta wasikar ga mambobin majalisar baki ɗaya.
Dama dai tun a ranar Juma’a ne 19 Ga Nuwamba, Majalisar Dattawa ta aika wa Buhari da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe ɗin.
A cikin doguwar wasiƙar da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ya karanta, Buhari ya bayyana dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu don ya zama doka.
Buhari ya ce ya karɓi shawarwari daga Ma’aikatun Tarayya, Ɓangarorin Hukumomi da Cibiyoyin Gwamnati.
Daga nan ya bayyana batun kuɗaɗe da batutuwan shari’u a matsayin dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu.
“Idan aka yi wa dokokin zaɓen kwaskwarima, to karya karsashin dimokraɗiyya kenan. Wannan kuwa shi ne ‘yancin da kowace jam’iyya mutum ya ga dama ya shiga ya zama mamba.
“Sai dai kuma a shekara mai zuwa majalisa za ta iya zaɓen hanya mafita idan an dawo daga hutun ƙarshen shekara.
Makonni biyu da su ka gabata ne wannan jarida ta buga labarin cewa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta aika wa Fadar Shugaban Kasa wasiƙar amincewa da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe.
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta aika wa Fadar Shugaban Ƙasa wasiƙar da batutuwan da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe ya ƙunsa.
Sai dai kuma INEC ta shawarci Shugaba Muhammadu Buhari ya tuntuɓi jam’iyyun siyasa da ɓangarorin jami’an tsaro, dangane da kudirin da aka shigar cewa zaɓen ‘yar-tinƙi jam’iyyu za su riƙa yi a wurin zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara.
A ranar 29 Ga Nuwamba ce Majalisar Dattawa ta aika wa Shugaba Buhari Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe, wanda shi kuma a bisa doka, ya na da kwanaki 30 kacal da zai ɗauka ya sa wa ƙudirin hannu, domin ya tabbata doka kenan.
Shi dai wannan sabon ƙudiri, matsawar Shugaba Buhari ya sa masa hannu, to ya shafe Dokar Zaɓen ta 2010 kenan, wadda ita ce aka yi wa kwaskwarima.
A cikin kwaskwarimar dai an nemi a riƙa yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen fitar da ‘yan takara.
Sai kuma batun suka sakamakon zaɓe ta yanar gizo da sauran na’urori da kafafen sadarwa na zamani.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ibrahim Gambari ne ya rubuta wa INEC wasiƙa, inda ya nemi hukumar ta rubuto shawarwari ga Buhari, kan batutuwan da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe su ka ƙunsa.
Gambari ya shaida wa INEC cewa kada shawarwarin su wuce ranar 3 Ga Disamba.
Batun a koma yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen zaɓuka na fidda-gwanin takarar jam’iyyu ya haifar da ka-ce-na-ce a cikin jam’iyyar APC mai mulki. Yayin da ‘yan majalisa waɗanda mafi rinjaye ‘yan APC ne, su da ɓangaren Bila Tinubu ke goyon bayan ‘yar-tinƙe, su kuma yawancin gwamnoni sun fi so a bar tsarin yadda ya ke, wato wakilai tun daga mazaɓu har zuwa sama su riƙa yin zaɓen fidda-gwani.