• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya

    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Dalilin da ya sa gwamnatin Najeriya ta ayyana ‘yan bindiga cewa ‘yan ta’adda ne

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
January 6, 2022
in Babban Labari
0
‘Yan bidiga sun bi Matawalle har Maradun sun sace daliban makarantar sakandare da rana tsaka

Gunmen-on-Motorbikes

Gwamnatin Najeriya ta ayyana wasu gungun ‘yan bindiga biyu da suka addabi Arewa maso Yammacin ƙasar cewa ‘yan ta’adda ne.

An raɗa masu sunan ne tare da duk wasu ƙungiyoyin da ke aikata wasu muggan laifuka masu nasaba da irin hare-haren da su ke kaiwa.

Raɗa wa ‘yan bindiga suna ‘yan ta’adda ya biyo bayan umarnin da Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta bayar a cikin watan Nuwamba, 2021 cewa Gwamnati ta ayyana ‘yan bindiga cewa ‘yan ta’adda ne.

Wannan sanarwa ta Gwamnatin Tarayya na cikin wata takarda da Kakakin Yaɗa Labaran Ministan Harkokin Shari’a, mai suna Umar Gwandu ya raba wa manema labarai a ranar Laraba, a Abuja.

“Wannan takarda ta zama shaidar cewa Gwamnatin Tarayya ta ayyana ‘yan bindiga da ‘yan ta’adda cewa ‘yan ta’adda ne, su da duk wasu ƙungiyoyin da ke aikata ɓarna irin ta su.”

Dama a ranar 29 Ga Nuwamba ne gwamnatin tarayya ta amince za ta ayyana su da suna ‘yan ta’adda, bayan kotu ta bayar da umarni.

An yi ta ƙorafe-ƙorafen neman gwamnati ta ayyana su ‘yan ta”adda, har dai a baya Ministan Tsaro ya fito ya faɗi abin da ya hana Gwamnatin Tarayya ayyana cewa ‘yan bindiga ‘yan ta’adda ne.

A wancan lokacin, Gwamnatin Tarayya ta bayyana cewa ba haka kawai gabagaɗi ake fitowa a ayyana cewa ‘yan bindiga su ma ‘yan ta’adda ne ba.

Ministan Harkokin Tsaro Bashir Magashi ne ya bayyana haka, tare da cewa akwai matakan da ake bi, kuma ko an bi su ɗin, to sai an tabbatar da kammaluwar su sannan za a ayyana cewa ‘yan bindiga ma ‘yan ta’adda ne.

Magashi ya yi wannan furuci a lokacin da ya kai ziyarar gani da idon irin ci gaban da ake samu a filin dagar yaƙi da Boko Haram a Barno.

Ya na tare da rakiyar Babban Hafsan Tsaron Ƙasa, Lucky Iraboh da sauran manyan hafsoshin ƙasa, ruwa da na sama.

Ya kuma gaba da manyan kwamandojin yaƙi na Arewa maso Gabas, wato ‘Threater Commanders’, tare da nuna gamsuwa da irin ƙoƙarin su da nasarorin da ake kan samu a yanzu.

Magashi ya yi wannan bayani ne biyo bayan tambayoyin da manema labarai su ka yi masa a Maiduguri, dangane da tsaikon da ake samu wajen ƙin kiran ‘yan bindiga da suna ‘yan ta’adda da Gwamnatin Tarayya ta ƙi yi.

Cikin makon jiya ne Shehin Malami Ahmad Gumi ya ce “za a yi da-na-sani idan Buhari ya raɗa wa ‘yan bindiga sunan ‘yan ta’adda.”

Babban malamin nan na Kaduna kuma wanda ya riƙa kurɗa-kurɗar shiga wurin ‘yan bindiga, Sheikh Ahmed Gumi, ya gargaɗi Shugaba Muhammadu Buhari da Gwamnatin Tarayya cewa kada su ayyana sunan ‘yan bindiga su ce musu ‘yan ta’adda.

Duk da kashe-kashe da garkuwa da mutanen da ‘yan bindiga ke yi, Gumi ya ce za a yi da-na-sani idan aka yi amfani da dokar ƙasa aka kira su ‘yan ta’adda.

Gumi wanda tsohon soja ne, kuma likita, ya daɗe ya na kamfen ɗin neman a yi wa Fulani ‘yan bindiga afuwa.

Ya shiga wurin ‘yan bindiga a dazukan Kaduna, Neja, Katsina, Sokoto da Zamfara. Kuma ya je jihohin inda ya gana da gwamnoni da gaggan gogarman ‘yan fashin daji masu garkuwa da mutane, da nufin a samu maslahar magance matsalolin da ke addabar yankunan.

Ko kwanan nan Gwamnan Katsina da na Kaduna sun nemi a bayyana ‘yan bindiga cewa ‘yan ta’adda ne, domin sojoji su samu cikakkiyar damar murƙushe su.

Sai dai Gumi a cikin wani bayani da ya wallafa a shafin sa na Facebook, ya yi babban kuskure ne idan aka bayyana ‘yan bindiga cewa ‘yan ta’adda ne.

Duk da ya nuna cewa su ma ‘yan bindiga su na kisa da ɓarnatar da dukiyar jama’a da garkuwa da mutane, to amma siyasa ta shiga cikin zukatan jama’a, musamman masu cewa su ma ‘yan bindiga ai ‘yan ta’adda ne.

Ya yi tsokaci kan yadda ‘yan bijilante ke kashe Fulanin da ba su ji ba, ba su gani ba, su ce duk ‘yan bindiga ne, abin da Gumi ya ce hakan kan tunzira sauran su shiga ƙauyuka kisan ramuwar-gayya.

Gumi ya bayyana irin ƙoƙarin da ya yi har ya sa wasu Fulani ‘yan bindiga masu yawa su ka tuba, su ka daina.

“Sai dai abin takaici, ba ni da masu taya ni wannan mawuyacin aiki da nake yi, maimakon haka ma, sai tulin masu gaba da ni na ke ƙara samu a kullum.”

Ya yi fatan a samu wani limamin Kirista na Igbo da ka Yarabawa su je su lallashi Nnamdi Kanu da su Sunday Igboho masu son ɓallewa daga Najeriya.

Ya ce idan su ka wayar wa magoya bayan su kai, za a samu maslahar zamantakewa tare da juna a matsayin mu na ƙabila daban-daban masu zaune a ƙasa ɗaya.

Ya ce malaman addini za su iya taka muhimmiyar rawa inda tsarin da babu addini ba zai iya yin tasiri ba.

Sai dai ya nuna takaicin maimakon jama’a su tashi tsaye a kwantar da wannan mummunar fitina, sai kowa ya yi zaman sa cikin ɗaki. Ya dararrashe ya na ta watsa bayanai barkatai waɗanda ba za su taɓa zama mabuɗin kawo ƙarshen fitintinu ba.

A ranar Lahadi ce dai Buhari ya bayyana cewa ‘yan bindiga da ba su da bambanci da Boko Haram.

Duk da dai har yau Shugaba Buhari bai fito ya bayyana ‘yan bindiga cewa su ma ‘yan ta’adda ne kamar yadda ake kiran ‘yan Boko Haram ba, a ranar Lahadi ya bayyana cewa “a wani ɓangaren ‘yan bindiga ba su da wani bambanci da ‘yan Boko Haram.”

Kakakin Yaɗa Labarai na Shugaba Buhari, Garba Shehu ne ya bayyana haka, a ranar Lahadi, bayan da wata mujalla mai suna The Economist, wadda ake bugawa a Landan ta buga labari cewa rashin tsaro a Najeriya ya ƙara dagulewa a ƙarƙashin mulkin Buhari.

‘Yan bindigar dai yanzu sun yi ƙarfin da har sun kai ga harbo jirgin yaƙin Najeriya ɗaya. Waɗanda Shehu ya ce sun yi ƙarfin tara kuɗaɗe da muggan makamai. “Kenan a nan ba su da wani bambanci ma da Boko Haram, waɗanda su a yanzu ma an yi masu tara-tara, an matse su a wuri ɗaya.”

‘Yan Najeriya da dama ciki har da Majalisar Dattawa da Gwamna El-Rufai na Kaduna, duk sun yi kira ga Buhari ya kira ‘yan bindiga cewa ‘yan ta’adda ne.

A martanin da Shehu ya yi masu, ya amince akwai ƙalubale daban-daban kan matsalolin tsaro a sassan ƙasar nan daban-daban.

Sai dai kuma ya ce duk Shugaba Buhari ya na ta ƙoƙarin magance matsalolin.

“Mujallar The Economist ta yi gaskiya, Najeriya na fuskantar matsalolin tsaro da dama. Sai dai a lura ba a cikin wannan gwamnatin matsalolin su ka faru ba. Wannan gwamnatin ce ma ke ta ƙoƙarin magance waɗannan ɗimbin matsalolin. “Alhali gwamnatocin baya babu wadda ta yi ƙoƙarin magance ko da matsala guda tal.” Inji Garba Shehu, cikin sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi, kuma ya aiko wa PREMIUM TIMES.

Ko a cikin makon da ya gabata, sai da Gwamna El-Rufai ya goyi bayan Majalisar Dattawa Tarayya domin kiran ‘yan bindiga da suna ‘yan ta’adda.

Gwamna Nasiru El-Rufai na Jihar Kaduna ya bayyana goyon bayan sa ga Majalisar Tarayya, wadda ta yi kira ga Gwmnatin Tarayya cewa ta shaida wa duniya ‘yan bindiga su ma ‘yan ta’adda ne kawai.

El-Rufai ya ce idan aka bayyana cewa ‘yan bindiga su ma ‘yan ta’adda ne, to hakan zai ƙara zaburar da sojoji su darkake su a duk inda su ke, su na yi masu kisan kan-mai-uwa-da-wabi, ba tare da tsoron ƙorafe-ƙorafe daga bakunan ƙungiyi kare haƙƙi na kasashen duniya ba.

Tags: 'Yan BindigaAbujaHausaKadunaKatsinaLabaraiMaharaNejaNewsPREMIUM TIMESSokoto
Previous Post

Bayan gwabza arangama, Gwamnan Gombe da Sanata Goje sun sasanta saɓanin su

Next Post

Dalilin da ya sa ba zan tsoma baki a saki Nnamdi Kanu ba -Buhari

Ashafa Murnai

Ashafa Murnai

Next Post
Nnamdi-Kanu

Dalilin da ya sa ba zan tsoma baki a saki Nnamdi Kanu ba -Buhari

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • RAƊAƊIN CIRE TALLAFIN FETUR: ‘Dama can babu ba a ware kuɗin tallafin fetur a Kasafin Kuɗin 2023 ba’ – Kyari, Shugaban NNPCL
  • SHARI’AR ZAƁEN SHUGABAN ƘASA: Tinubu da INEC sun ƙi amincewa da tulin kwafe takardun da Atiku ya kwafo daga iReV
  • GANAWAR TINUBU DA NLC: Ƙungiyar Ƙwadago ta ce a tilas a soke ƙarin kuɗin mai, an shammaci ‘yan Najeriya
  • HAJJI 2023: Gwamnatin Filato ta bar mahajjatan jihar su na hajijiya a Madina
  • Kada ku tausaya min don na faɗi zaɓen Sanatan Zamfara – Sanata Marafa

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.