A wani ƙwarya-ƙwarya kuma taƙaitaccen cimma matsaya da Majalisar Dattawa ta yi a ranar Talata, ta sake yi wa Ƙudiri na 84 na Dokar Gyaran Zaɓe Kwaskwarima.
An yi kwaskwarima ɗin ce ta yadda idan Shugaba Muhammadu Buhari ya sa mata hannu, za ta bai wa jam’iyyun siyasa damar kowace ta bi tsarin da ya fi daidai a gare ta wajen zaɓen fidda gwani.
A cikin ƙudirin gyaran dokar zaɓen dai wanda Majalisar Dattawa ta sa wa hannu cikin 2021, sun rattaba cewa zaɓen fidda gwanin kowace jam’iyya zai kasance na ‘yar-tinƙe ce.
Sai dai kuma Shugaba Muhammadu Buhari bai amince da wannan ƙudirin ba.
Dalili kenan ya maida wa majalisa domin ta yi masa kwaskwarima.
Yayin da Majalisar Dattawa ta amince da zaɓen kai-tsaye ko ‘yar tinƙe ko kuma tsayar da ɗan takara a bisa tsarin yarjejeniyar amincewa, ita kuwa Majalisar Tarayya ba ta amince da fitar da dan takara ta hanyar cimma yarjejeniyar tsayar da mutum ɗaya ba tare da zaɓe ba (wato consensus candidate).
Farkon makon jiya ne Majalisar Dattawa ta yi wa Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe Kwaskwarima kamar yadda Shugaban Muhammadu Buhari ya nemi ta yi, kafin ya sa mata hannu
Gyare-gyaren Da Majalisar Dattawa Ta Yi Wa Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe:
Majalisar ta fara yin gyaran gaggawa kan Ƙudiri na 87, wanda ya yi magana kan irin zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara daga kowace jam’iyyar siyasa.
A yanzu an amince kowace jam’iyya ta zaɓi gwanayen ta bisa tsarin ‘yar tinƙe, ƙato-bayan-ƙato ko zaɓen game-gari.
Da farko dai Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe ya amince a yi zaɓen kai-tsaye, ba na wakilan jam’iyya ba, wato ‘delegates’.
Wannan tsari ne ake kai a ƙasar nan, wanda kuma ƙoƙarin kawar da shi a zaɓen 2023 bai yi nasara ba, biyo bayan fatali da tsarin zaɓen kai-tsaye da Buhari ya yi bisa dalilin cewa zai ci maƙudan kuɗaɗe wajen gudanarwa.
An amince da Ƙudiri na 84, wanda ya bada damar ko jam’iyya ta yi zaɓen kai-tsaye ko kuma tsarin wakilan jam’iyya, wato ‘delegets’.
An kuma amince da Ƙudiri na 84(2), wanda ya bada damar cewa jam’iyya za shirya zaɓen fidda gwani ta hanyar wakilai, ko kumà a cimma yarjejeniyar tsayar da wani ba tare da an yi zaɓe ba.
A zaɓen fidda-gwamnin ɗan takarar shugaban ƙasa, an gindaya cewa tilas sai an yi Taron Gangamin Jam’iyya a kowace jiha 36 da Abuja FCT, domin wakilan jam’iyya daga mazaɓu su yi zaɓen ‘yan takara.
Haka nan kuma ƙudirin ya ce za a shirya babban zaɓe na ƙasa, inda za a jaddada ɗan takarar da ya fi sauran ‘yan takara yawan ƙuri’u.
Premium Times Hausa ta buga labarin cewa, Sanata Ahmad Lawal ya ce “za mu yi wa Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe Kwaskwarima, mu sake aika wa Buhari ya sa hannu.’
A labarin, Shugaban Kakakin Majalisar Dattawa Ahmad Lawan, ya bayyana ce Majalisar Dattawa da Majalisar Tarayya kowace za ta yi zaman yi wa Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe Kwaskwarima a ranar Laraba, domin a cire wuraren da ake tankiya a kai, sannan su sake aika wa Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannu.
Lawan ya yi wannan ƙarin haske ne a ranar Talata da dare, yayin da ya ke ganawa da manema labarai, bayan ganawar da ya yi a keɓance tare da Shugaba Muhammadu Buhari.
Lawan ya ce za su yi haka ne domin a samu damar sa wa sauran ƙudirorin dokar hannu su zama doka, yadda za a gyara tsarin zaɓe a 2023.
Shugaban Muhammadu Buhari dai ya ƙi sa wa ƙudirin hannu saboda dalilan da ya kawo.
Bayan an yi ta ce-ce-ku-ce ne kuma sai Buhari ya ce zai iya sa wa ƙudirorin hannu su zama doka, amma idan an cire wuraren da ake tankiya a ciki.
Lawan ya ce, “Idan Allah ya yarda a ranar Laraba, 18 Ga Janairu Majalisar Tarayya da Majalisar Dattawa kowace za ta yi zaman gyaran ƙudirorin, ta yadda za a gaggauta aika wa Shugaban Ƙasa ya sa hannu.