• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Buhari-signing-2020-budget

    Gwamnatin tsohon shugaban kasa Buhari ta sanar da sabbin nade-nade a daidai ana rantsar da Tinubu shugaban kasa

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    Minista Sadiya ta miƙa ragamar Ma’aikatar Harkokin Jinƙai ga Babban Sakatare

    2015-2023: ‘Na yi sukuwa ta lafiya, na kai zamiya lafiya’ – Buhari

    BANKWANA DA BUHARI: ‘Tinubu yau mafarkin ka ya zama gaskiya, Allah ya sa ka kai Najeriya fiye da inda na kai ta’ – Nasihar Buhari ga Asiwaju

    Tsakanin Sanata Barau da Gwamna Ganduje, Daga Jaafar Jaafar

    Ba zan jira Litinin ba, tun Lahadi zan mika mulki ga Abba Gida-Gida in kama gaba na – Ganduje

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANTSAR DA TINUBU: Kotun Koli ta yi watsi da karar rashin cancantar Tinubu shiga zaɓen 2023

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    RANAR RANTSAR DA TINUBU: Za mu hana makiyaya karakaina da shanu a cikin Abuja – Shugaban Miyetti Allah

    An Karrama gidan Jaridar PREMIUM TIMES da kyauta mafi daukaka a aikin Jarida na kasar Amurka

    BA DA MU BA, TAYA ƁERA ƁARI: PREMIUM TIMES ta nesanta kan ta daga ƙungiyar da ta jona sunan ta a shirya taron karrama wasu mutane

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    KIRAN RUWA: ‘Ka wa Allah ka ɗaga mana kafa, kada ka kwace mana filayen mu har 9 da ka kunno kai a kan su – Makarfi ga El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

    ‘Ni da Wike kaman ‘Yan biyu ne, muna tsage gaskiya komai dacin ta’ – El-Rufai

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    QATAR 2022: Ko ƙasashen Afrika za su fidda nahiyar jin kunya a duniyar ‘yan ƙwallo

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    DAGARGAZA ARGENTINA: Ƙasar Saudiyya ta ba da hutun kwana Ɗaya a wataya

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

    QATAR 2022: 2:1: Saudiyya ta kafa tarihin karya gadara da tutiyar buga wasan Agentina 36 a jere babu rashin nasara

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    BIDIYO: NAJERIYA @62: Ra’ayoyin ‘yan Najeriya game da mulkin Buhari a tsawon shekaru 7 da suka gabata

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Buhari bai san ƴan ta’adda sun fidda bidiyon da suka ce sai sun sace shi da ni ba sai da na ziyarce shi – El-Rufai

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    Dalilin da ya sa na raɗa wa wasu fitattun gine-gine, da titunan jihar Kaduna sunayen wasu fittattun ƴan asalin jihar

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a  Kano

    HOTUNA: Ɗan Autan marigayi tsohon sarkin Kano Ado Bayero, Mustapha Ado Bayero, ya auri mata biyu ranar Asabar a Kano

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

    BIDIYO: An yi wa ɗan takarar mu murɗiya a zaɓen fidda gwani na APC a Legas – Masu zanga-zanga

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

TALLAFIN MAN FETUR: BUHARI, IMF, PIA da Tallakan Nijeriya, Daga Ahmed Ilallah

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
December 14, 2021
in Ra'ayi
0
TALLAFIN MAN FETUR: BUHARI, IMF, PIA da Tallakan Nijeriya, Daga Ahmed Ilallah

Babban kalubale wanda a kullum yake addabar shugabannin Nijeriya, musamman a fannin tattalin arziki, bai wuci ta yadda bunkasar tattalin arziki wanna kasar baya tasiri a rayuwar talakan Nijeriya ba, ko nawa girman tattalin arzikin nijeriya ya kai wato GDP ba a ganin wani chanji a wajen talakan kasar nan. Kai duk lokacin da a kace man fetur ya tashi a kasuwar duniya tofa shi kuma tallakan Nijeriya ya shiga tashin hankali da jimamin za a kara masa firashi man da yake saya.

Wai shin kuwa gwamnatin Baba Buhari da hukumomin tattalin arziki na duniya suna nazari kuwa a kan yadda rayuwar talakawan Nijeriya take, kafin tursa sa su akan wata manufa akan arzikin kasarsu? Koda ance ana saida man fetur da araha a Nijeriya sabanin sauran kasashe masu arzikin man fetur, to yana da kyau ayi la’akari da talauchin da yayi way an kasar katutu.

A misali, bincike ya nuna duk duniya dan Nijeriya ne kadai ya kan kashe kusan duk abin da ya samu akan abinci, saboda tsananin talauchi. Matsakaicin mutum dan Nijeriya yakan kashe kashi 65% na kudin da ya samu wajen sayen abinci kadai, wanda wannan yake kara tura yan kasar cikin kangin talauchi. Amma a kasashe kamar Amurka su kan kashe 6.4%, Birtaniya 8.2%, Canada 9.1%, Australia 9.8% kacal ne a kan abinci. Da wuya wani yace an yid an Nijeriya adalchi in har aka hada shi da irin wannan kasashe wajen sayen arzikin da ke kasarsa. Shi kansa Bankin Duniya (World Bank) a wannan shekarar ya fidda kididdiga cewa farashin abinchi a Nijeriya ya karu da 22%, wanda ya sake sanya al’umma cikin talauci.

A bangren sufuri kuwa, wanda ke zaune a kasar England zai iya zuwa yayi aiki a kasar Germany ko France ko Belgium ya dawo ya kwana a gidan sa, ta hanyar jirgin kasa, amma a Nijeriya babu kykyawan tsari na sufuri, misali daga Kano zuwa Legas ko Abuja ko Patacol. Yan Nijeriya sun fi kowa mutuwa a duniya ta hanyar hatsarin mota, sakamakon yin amfani da kana motocin da bai kamata a yi sufuri da suba. Talauchi da rashin kudi kan sanya pasinjoji cunkusuwa sama da mutane gome a mota mai cin mutun hudu kachal, amma a kasashen da suka da kyakkyawan shugabanci sun tanaji motoci na sufuri don kaucewa hatsura.

A duk masu arzikin man fetur a duniya, kama da kasashen da ke cikin kungiyar OPEC Nijeriya ce kadai bata iya tace man fetur a kasarta, wannan ba komai bane face gazawar shugabanci da shugabanni. Shekaru da yawa Nijeriya ta samu kanta cikin matsalar tacewa da sayar da man fetur, kasancewar yana da ga cikin babban abun bukata ga yawan al’ummar wannan kasar, kasancewar babu kyawawan tsari da shugabannin kasar nan suke samar a fannin tattalin arziki da kawar da talauchi a tsakinin yan kasa, babban al’amari ma babu wani kykkyawan tsari na sufuri, wanda shine ganshiki amfani da man fetur.

Matsalar man fetur da tallafin man fetur ya zama wata siyasa da masu neman mulki ke amfani da shi wajen neman a zabesu, wanda kawai ana kokuwar neman iko ne ba tare da shirin warware wannan matsalar ba, da zarar an samu nasara, sai a dulmiya cikin matsalar fiye da ta baya, ana maganin kaba kayi na kumbura.

Gwamnatin shugaba Buhari da jama’iyar APC, sun sami galabar cin zabe a shekarar 2015 ne, bisa yayatu tabbarbarewar tsaro da kuma yunkurin cire tallafin man fetur da gwamnatin PDP da shugaba Goodluck Jonathan tayi yunkurin yi a wannan lokacin a shekara ta 2012. A wannan lokacin kungiyar ‘Yan Kwadago sun jagoranci zanga-zagar da ake kira ‘Occupy Nigeria’ wanda harda shugaba Buhari da sauran jagororin jami’iyun adawa a wannan lokacin sun hallata, kuma wannan bijerewar ta yan kasa ta hana kara kudaden man fetur din. Amma da Buhari yahau mulki, me ne ne ya biyo baya?
Wai ma yasa ne, kowane lokaci kasashen turawa da hukumomin su irin su IMF, basa kawo wa Nijeriya wani tsari ko tilasta su akan wani tsari, sai lokacin da kasar take kan wani bigire na rashin zaman lafiya? Ko kuma sai muna daf da mu shiga zabe, duk da sun san cewa, wannan tsarin zai iya kawo fitina, koma ya sanya kasar cikin wani yanayi.

A shekarar 2012 Nijeriya na tsaka da fitinar Boko Haram an samu irin wanna yanayin na cire tallafi da kara kudin mai, kamar yadda na fada a sama, wanda da kyar kasar nan ta sami kanta, har ma wasu turawan na harsashen bajewar kasar kafin zaben 2015, amma Allah ya karyata su.

Wai wace ce hukumar IMF ne, wanda shugabannin muke tsoro kamar Allah, wanda kullum tsare tsarenta ya kan sake dunkufar da talaka ne kawai, sannan ya share musu hanyar sake mallakar mu ta fuskar tattalin arziki.

A takaice wannan hukuma ta IMF an samar da ita ne bayan an gama yakin duniya na biyu (second world war), Kasar Amurka da kasar Bitaniya ne suka kan gaba wajen kafa wannan hukumar da takwararta ta World Bank, wanda ita hukumar IMF tafi maida hankali wajen sanya wa kasashe ka’idodi na tafikad da tattalin arzikinsu wanda zai dace da muradin kasar Amurka, wato economic policies.

Babban Ma’ajin Amurka (US Treasury Secretary) Harry Dexter White da kuma masanin tattalin arzikin kasar Birtaniya wato John Maynard Keynes, wanda kowanan su ya wakilci kasar sa, su suka tsara da samar da wadan nan hukumomi na IMF da World Bank.

A takai ce wannan hukuma ta IMF babbar makiya ce ga kasashe masu tasowa, musamman na Africa domin yi tarnaki na bunkasa tattalin arzikin su dama barin su su zau na lafiya, ta hanyar kawo musu tsare-tsare da ya sabawa muradun al’umar su.

IMF ta kasance kamar yar sandar duniya ta fnnin tattalin arziki, musamman ka kasashe na bakar fata. Wannan hukuma kawai tanayiwa kasar Amurka ne aiki, wannan ya sanya basa kula da yadda kasa ta ke ciki wajen tilasta musu bin tsari da bai dace da suba.

A wani hannun su kuma shugabannin mu, suna da lalaci, rashin kwarewa a kan matsalolin al’umar su, musamman a fannin tattalin arziki da bunkasa shi. Shugabannin kasashen mu sun fi son mulki da dawamma a kan mulki fiye da bautawa al’umar su, sun gwamce da sharholiya da kasha kudaden talakawa a kan biyan bukatun su, maimakon gina musu kykkywan tsari don yaye musu talauchi da samar musu yalwatacciyar rayuwa.

Ba kawai hukumar IMF fa, it ma sabuwar dokar man fetur da shugaba Buhari ya sanya wa hannu a wannan shekarar wato Petroleum Industrial Bill (PIA), kusan ta damula siyasar tallafin man fetur, wanda wannan dokar ta bayan gida ta cire hannun gwamnati akan harkar man fetur, yadda a yanzu hukumar NNPC ta koma NNPC Limited, wanda ko da a yanzu ta soma ikirarin cin riba, wanda a baya bata iya lissafa riba koma faduwa, wanda a takaice, tabar kasuwa tayin halinta a game da man fetur.

Wannan doka ta nuna cewa a hankali gwamnati zata zare hannun ta a kan man fetur a wannan kasar. Wanda wannan ya sanya hukumar NNPC din ta yi nuni da cewa duk mai adawa da cire tallafin man fetur, to ya makara, har su kan su kungiyar ‘Yan Kwadagon, domin sunce da basu bari an aiwatar da dokar ba tun daga majalissar dokoki ta kasa, kafin ta samu sahalewar shugaban kasa. Wanda yanzu suna ganin karshen tika tika tik, akan cire tallafin man fetur.

Koma bai ke faruwa ya kamata Shugaba Buhari ya tuna alkawarin sa da talakawan Nijeriya, wanda su su ka kawo shi kan mulki, bacin yayi karo biyar yana faduwa, na rage musu kuncin rayuwa da basu zaman lafiya. Ya kuma zama dole mahukunta suyi nazari da kasar su, al’umar su kafin kawo ko wane tsarin musamman a irin wannan lokaci.

alhajilallah@gmail.com

Tags: AbujafeturHausaMaiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Daga 2022 daliban da suka yi rigakafin korona ne za su yi wa kasa hidima na NYSC

Next Post

An tsinci gawar Ɗan majalisan Kaduna kwanaki biyu bayan harin ƴan bindiga a Titin Zaria-Kaduna

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
An tsinci gawar Ɗan majalisan Kaduna kwanaki biyu bayan harin ƴan bindiga a Titin Zaria-Kaduna

An tsinci gawar Ɗan majalisan Kaduna kwanaki biyu bayan harin ƴan bindiga a Titin Zaria-Kaduna

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Abubuwa 12 Da Suka Hana A Ga Ƙoƙarin Mulkin Buhari
  • YUNƘURIN BALLEWA DAGA NAJERIYA: Yadda tsagerun Yarabawa suka kama Gidan Radiyon Gwamnatin Tarayya, kwana ɗaya kafin rantsar da Tinubu
  • RA’AYIN PREMIUM TIMES: Shekarun Mulkin Buhari: An sake ɓata goma, biyar ba ta gyaru ba
  • Zan yi tafiya da kowa da kowa a gwamnati na – Uba Sani
  • TINUBU: Abinci zai wadata cikin farashi mai sauƙi

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.