Majalisar Dattawa ta yi wa Kasafin Kuɗaɗe na 2022 ƙarin naira biliyan 700.
A yanzu kasafin ya tashi daga naira tiriliyan 16.4 ya koma naira tiriliyan 17.12.
Wannan ƙarin ya zo ne ƙasa da kwana ɗaya bayan Majalisar Tarayya ta miƙa kasafin.
Haka nan kuma Majalisar Dattawa ɗin dai ta maida cewa za a yi kasafin ne daidai da dalar Amurka 62, maimakon dala 57 da Buhari ya yi kasafin da farko.
Dalilin yin haka kuma shi ne saboda farashin gangar ɗanyen mai ta ƙaru bayan Buhari ya gabatar da kasafin a kan dala 57.
Sannan kuma an amince za a riƙa haƙo gangar ɗanyen mai miliyan 1.86 a kowace rana a Najeriya.
Majalisar Dattawa ta yi ƙari kan kasafin kuɗaɗen ne bayan da wasu ma’aikatu da hukumomi su ka gabatar wa majalisa ƙarin buƙatun kuɗaɗe, waɗanda ba a saka su a cikin Kasafin 2022 ba.
Ma’aikatun da su ka nemi kuɗaɗen sun haɗa da Ma’aikatar Ayyuka da Gidaje, Hukumar Zaɓe ta Ƙasa, INEC, wadda ta nemi naira biliyan 304 domin shirya zaɓen 2023. Sai kuma Hukumar Tsaro ta Sojoji, Hukumar Ƙidaya ta Ƙasa, Ma’aikatar Harkokin Noma da Raya Karkara, Hukumar Leƙen Asiri, Ayyukan Majalisar Dattawa da Tarayya a Mazaɓu.
Sai kuma Ma’aikatar Ilmi, Ma’aikatar Agaji, Jinƙai da Inganta Rayuwa da kuma Ma’aikatar Harkokin Ruwa.
Discussion about this post