Wani babban lauya, Jiti Ogunye ya bayyana cewa dokar kasa ta ba majalisar damar rattaba hannu a Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe da shugaban Kasa ya maida musu da ita.
Jiti ya ce duka korafin da Buhari ya bayyana cewa su ne suka sa ba zai saka hannu a dokar ba dalili bane da zai sa ya ki saka hannu a dokar.
” Da ma a cikin makon jiya, shugaban majalisar Dattawa, Ahmed Lawan ya yi kurin cewa majalisar ba ta jeka na yi ka bane, ‘yan abi sarki asha kida, to ga dama ta samu yanzu sai su nuna bajintarsu su rattaba wa kudirin hannu idan har da gaske suke domin hujjojin da buhari ya bayyana na son rai ne ba don ci gaban siyasar Najeriya ban.
” Yaya za ce wai saboda zaben ‘yattinke ne zai sa Buhari ya ki saka wa kudirin gyarar hannu. Amma kuma a baya shine ya ke kukan dokar zabe na bukatar gyara wanda ya na daga cikin dalilin da ya sa ba a yi masa adalci ba a can baya a lokacin da yake takarar zama shugaban kasa a Najeriya.
Shugaba Muhammadu Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya wasiƙar sanar da su cewa bai yarda da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe na 2021 ba, don haka ba zai sa wa dokar hannu ba.
Fatali da ƙudirin na ciki wasiƙar da Buhari ya aika wa Majalisar Dattawa da ta Tarayya a ranar Talata ɗin nan, kuma majalisun biyu duk su ka karanta wasiƙun na shi a zaman ranar Talata ɗin nan.
Shugaban Majalisar Dattawa Ahmad Lawan da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ne su ka karanta wasikar ga mambobin majalisar baki ɗaya.
Dama dai tun a ranar Juma’a ne 19 Ga Nuwamba, Majalisar Dattawa ta aika wa Buhari da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe ɗin.
A cikin doguwar wasiƙar da Kakakin Majalisar Tarayya, Femi Gbajabiamila ya karanta, Buhari ya bayyana dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu don ya zama doka.
Buhari ya ce ya karɓi shawarwari daga Ma’aikatun Tarayya, Ɓangarorin Hukumomi da Cibiyoyin Gwamnati.
Daga nan ya bayyana batun kuɗaɗe da batutuwan shari’u a matsayin dalilan sa na ƙin sa wa ƙudirin hannu.
“Idan aka yi wa dokokin zaɓen kwaskwarima, to karya karsashin dimokraɗiyya kenan. Wannan kuwa shi ne ‘yancin da kowace jam’iyya mutum ya ga dama ya shiga ya zama mamba.
“Sai dai kuma a shekara mai zuwa majalisa za ta iya zaɓen hanya mafita idan an dawo daga hutun ƙarshen shekara.
Makonni biyu da su ka gabata ne wannan jarida ta buga labarin cewa Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta aika wa Fadar Shugaban Kasa wasiƙar amincewa da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe
Hukumar Zaɓe ta Ƙasa (INEC), ta aika wa Fadar Shugaban Ƙasa wasiƙar da batutuwan da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe ya ƙunsa.
Sai dai kuma INEC ta shawarci Shugaba Muhammadu Buhari ya tuntuɓi jam’iyyun siyasa da ɓangarorin jami’an tsaro, dangane da kudirin da aka shigar cewa zaɓen ‘yar-tinƙi jam’iyyu za su riƙa yi a wurin zaɓen fidda-gwanin ‘yan takara.
A ranar 29 Ga Nuwamba ce Majalisar Dattawa ta aika wa Shugaba Buhari Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe, wanda shi kuma a bisa doka, ya na da kwanaki 30 kacal da zai ɗauka ya sa wa ƙudirin hannu, domin ya tabbata doka kenan.
Shi dai wannan sabon ƙudiri, matsawar Shugaba Buhari ya sa masa hannu, to ya shafe Dokar Zaɓen ta 2010 kenan, wadda ita ce aka yi wa kwaskwarima.
A cikin kwaskwarimar dai an nemi a riƙa yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen fitar da ‘yan takara.
Sai kuma batun suka sakamakon zaɓe ta yanar gizo da sauran na’urori da kafafen sadarwa na zamani.
Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Ƙasa, Ibrahim Gambari ne ya rubuta wa INEC wasiƙa, inda ya nemi hukumar ta rubuto shawarwari ga Buhari, kan batutuwan da Kudirin Gyaran Dokar Zaɓe su ka ƙunsa.
Gambari ya shaida wa INEC cewa kada shawarwarin su wuce ranar 3 Ga Disamba.
Batun a koma yin zaɓen ‘yar-tinƙi wajen zaɓuka na fidda-gwanin takarar jam’iyyu ya haifar da ka-ce-na-ce a cikin jam’iyyar APC mai mulki.
Yayin da ‘yan majalisa waɗanda mafi rinjaye ‘yan APC ne, su da ɓangaren Bila Tinubu ke goyon bayan ‘yar-tinƙe, su kuma yawancin gwamnoni sun fi so a bar tsarin yadda ya ke, wato wakilai tun daga mazaɓu har zuwa sama su riƙa yin zaɓen fidda-gwani.
Discussion about this post