A ranar Laraba ne Amaka Chinwendu ta kai kara ofishin ‘yan sandan jihar Ebonyi bayan mijinta ya gudu ya barta da ‘ya’yan su uku da suka haifa tare.
Amaka ta bayyana wa jami’an tsaron cewa ta fara samun matsaloli da mijinta ne tun bayan da suka yi gwaji aka gano cewa tagwaye ne a cikinta.
Ta ce mijinta Chinwendu Wako ya bayyana mata cewa a garin su Igbo-Etche dake karamar hukumar Etche al’adunsu sun haramta wa mace ta haifi tagwaye sannan muma haramun ne ko mai dalili ko matsala ayi wa mace fida wajen haihuwa.
“Na haifi ‘ya mace ta farko sannan tun da muka gano cewa ina dauke da cikin ‘yan biyu ne Chinwendu ya fara yi mini wulakanci da muzguna min.
“Chinwendu ya ce ba zai sake kula da ni ba idan ba na zubar da cikin da nake dauke da shi bane tun a wancan lokaci. Kuma haka ya rika gallaza min azaba ina hakuri har na haihu.
Amaka ta ce ta haifi mace da namiji sannan a yanzu haka watan su biyu.
Ta ce tun bayan da Chinwendu ya gudu ya barsu a asibiti ‘yan uwanta ne suke kula da ita.
Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Loveth Odah ta bayyana cewa rundunar za ta gudanar da bincike domin gano gaskiyar lamarin.
Discussion about this post