• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Ku fito ku ceci mutanen jihar Kaduna kamar yadda kuka yi a zaben majalisun Tarayya da na sanatoci – Isah Ashiru

    An yi mana kwange a hukuncin kotu, za mu daukaka kara – Ashiru

    SSS

    TAKE HAƘƘIN ƊAN ADAM: Yadda SSS suka riƙa faffalla min mari, suka ja ni ƙasa girrrr, don kawai na ce su bi doka – Lauya Ogbankwa

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    Muna ƙarancin malamai, a janye dokar hana ɗaukar sabbin malamai da gwamnatin tarayya ta ƙaƙaba – Jami’ar ABU

    TONON ASIRI: An kama wani Dagaci cikin gungun mahara a lokacin batakashi da ‘Yan sanda

    ‘Yan bindiga sun kashe mutum shida a Kaduna

    Almajirai

    UNICEF ta saka Almajirai sama da 20,000 cikin rajistar tsarin agaza wa marasa karfi a Katsina

    Majalisar Tarayya ta ce a soke ƙarin kuɗin makaranta da aka yi wa ɗaliban jami’o’i da na Kwalejojin Gwamnatin Tarayya

    KALUBALEN DA KE GABAN MAJALISAR WAKILAI TA ƘASA: Gaganiya da matsalar raɗaɗin tsadar rayuwa, matsalar tsaro da sauran su da ake fuskanta a kasa

    Yadda sojojin sama sun ragargaza sansanonin ‘yan bindiga a jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto da Kaduna

    RASHIN TSARO: Tinubu ya amince da sayo jiragen sama masu saukar ungulu 12 ga sojojin Najeriya – Lagbaja

    TA’ADDANCI A JIHAR NEJA: Yadda ƴan ta’adda su ka ratsa garuruwa, kafin su  kai wa sojoji da mobal farmaki

    Ƴan ta’adda sun gamu da fushin sojojin Najeriya, sojoji sun kashe 50 sun kama 60

    GRAINS MARKET AT KAFIN MADAKI DISTRICT IN GANJUWA

    Yari ya raba tallafin tirela 145 cike maƙil da buhunan masara 145 ga mabuƙata a Zamfara

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    Hukumar CAF za ta binciki yadda mahaifiyar ɗan wasa ta mutu cikin 1986, shi kuma ya ce atabau cikin 1990 ta haife shi

    A karo na Uku, Moroko za ta ɗauki baƙuncin gasar cin kofin kwallon ƙafa na nahiyar Afrika a Janairun 2025

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    NFF ta sake nada Chris Danjuma a matsayin kocin Falconets

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    DARAJAR ƘWALLON ƘAFA TA KOMA SAUDIYA: Karim Benzema zai riƙa ɗaukar albashin kusan Naira Biliyan 100 a shekara, a ƙungiyar Al-Ittihad

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    TSOHO MAI RAN ƘARFE: Obasanjo ya zura ƙwallaye uku a wasan sada zumuntar tsoffin ɗaliban sakandare

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    QATAR 2022: Yadda Croatia, ƙasa mai mutum miliyan 4 ta kori Brazil ƙasa mai mutum miliyan 216

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    AMBALIYAR QATAR 2022: Spain ta kori kociya Luis Enrique bayan ta kwashi buhun kunya a hannun Marocco

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2023: Yadda Walid, kociyan Morocco ya rikita duniyar ƙwallon ƙafa cikin watanni 4 kacal

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    QATAR 2022: Dukkan ƙasashen Afrika 4 da su ka taɓa kai wasan kaiwa ga na kusa da na ƙarshe, su na da tauraro a jikin tutocin su

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

    Abubuwan al’ajabi dangane da fatattakar da Morocco ta yi wa Spain daga Qatar 2022

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    BIDIYO: Yadda rufe iyakar Najeriya da Nijar, ya jefa mu cikin tsananin fatara, da halin kakanikayi a yankin Katsina – Saidu

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    Yadda SSS da Jami’an Gidan Kurkuku suka kwashi ‘yan kallo a kotu, saboda Emefiele

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ‘Duk wanda ya ci kuɗin Tallafin Korona a Jigawa sai ya amayo shi’ – Gwamna Namadi

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    BIDIYO: ALhazan Kano sun gama shiri tsaf don ‘Hawan Arafat’ – Alhussain Maiwada

    JERIN SUNAYE: Jami’o’i 51 da ba za su dauki dalibin da ya ci kasa da maki 180 a jarabawar JAMB ba

    TSARIN BAI WA ƊALIBAI RAMCE: Abubuwan da suka wajaba ɗalibai da iyaye su sani

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    Buhari ya tashi zuwa Saudiyya, zai yi Umra ta ƙarshe a matsayin sa na shugaban kasa

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Buri da fata na a 2023: Ra’ayoyin jama’a

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    BIDIYO: Ƙogon Al’ajabi, ƙogon Waraka, Ƙogon biyan bukata a jihar Enugu

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

    Mutanen Arewa na da alƙawari da sanin ya kamata, Tinubu za su yi saboda ƙauna da biyayyar da ya nuna wa Buhari – El- Rufai

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

BANKWANA DA 2021: Alƙawurra 10 da gwamnatin Buhari da Jam’iyyar APC mai mulki suka kasa cikawa daga 2015 zuwa 2021

Premium Times HausabyPremium Times Hausa
December 31, 2021
in Babban Labari, Rahotanni
0
Buhari Campaign

Buhari Campaign

Daga ranar Asabar, 1 Ga Janairu 2022, zai kasance shekara ɗaya tal ta rage wa Shugaba Muhammadu Buhari a kan mulki. Duk da saura shekara ɗaya da watanni biyar ya kammala wa’adin mulkin sa, a gaskiya watanni uku daga biyar ɗin duk a wurin kamfen ɗin sake zaɓe su ke tafiya. Ragowar watanni biyu kuma na tafiya ne wajen shirye-shiryen sauka daga mulki.

Buhari ya samu nasarar zama shugaba bayan ya ɗaukar wa ‘yan Najeriya alƙawurra da dama, na alwashin tsamo ƙasar nan daga cikin halin ƙuncin da masu adawa da PDP ke cewa Najeriya ta shiga a lokacin.

Tabbas kowa ya san a lokacin PDP an yi fama da matsaloli, musamman munanan hare-haren ƙunar-baƙin-wake a Arewacin ƙasar nan.

Alƙawurra 10 Da Har Yau Ke Rataye A Wuyan Buhari:

1. Korar Fatara Da Talauci: Gwamnatin Buhari ya ɓullo da shirye-shirye na raba wa talakawa kuɗaɗe, bayar da ramce ga manoma da samar wa matasa ayyukan N-Power. Sai dai kuma wasu tsauraran matakan da ya ɗauka, musamman kulle kan iyakoki da hana shigo da shinkafa, sun taimaka ƙwarai wajen ruruta tsadar kayan abinci a ƙasar nan.

Kusan duk wani nau’in kayan abinci da ake sayarwa kafin Buhari ya hau mulki cikin 2015, yanzu farashin sa ya nunka. Wani ma ya nunka sau uku ko sau huɗu.

2. Rashawa Da Cin Hanci: Irin yadda Ofishin Babban Mai Binciken Kuɗaɗe na Tarayya ke ci gaba da bankaɗo yadda ma’aikatun gwamnati da hukumomi da wasu cibiyoyi ke karkatar da kuɗaɗe, ya nuna har yanzu a gwamnatin Buhari kamar ta PDP, cike ta ke masu badaƙala.

Shi kan sa yaƙi da cin hancin a zamanin gwamnatin nan ya sha karo da samun cikas, inda aka riƙa zargin Ministan Shari’a Abubakar Malami, aka sallami tsohon Shugaban EFCC, Ibrahim Magu, kuma aka tsige Shugaban Kwamitin Yaƙi da Rashawa na Shugaban Kasa, wanda Buhari ya kafa a ƙarƙashin ofishin sa.

Da yawa dawo daga rakiyar yaƙi da ɓarayin gwamnati, ganin yadda da yawa waɗanda aka riƙa zagi a lokacin da Buhari ke kamfen, su ka koma APC har aka ba su muƙaman siyasa.

Har yau bayan shekaru bakwai, babu wani tsohon ministan PDP guda uku da ke tsare a kurkuku. Kuma babu gwamna uku gangariya da ke tsare a kurkuku. Kuma babu manyan ma’aikatan gwamnati 10 dindi waɗanda ke tsare a kurkuku.

3. Matsalar Tsaro: A gaskiya an samu ragin tashin bama-bamai bayan hawa mulkin Shugaba Buhari. To amma kuma har yanzu Boko Haram na ci gaba da kai munanan hare-hare a kan sojojin Najeriya. Har yau dai Boko Haram ke kai farmaki har sansanonin sojin mu.

Mafi yawan labaran da mu ke ji a Arewa maso Gabas, su ne Boko Haram sun kai wa Sojojin Najeriya hari, amma an fatattake su. Ba mu jin labaran sojoji sun kori Boko Haram, sun raka su har maɓuyar su, sun karkashe su a can.

Sannan kuma har yau Boko Haram na kai wa garuruwa da ƙauyuka hari.

3a. Bala’in ‘Yan Bindiga: Maimakon a ga Buhari ya tashi tsaye haiƙan ya magance matsalar ‘yan bindiga, sai ya kasance bala’in a kullum sai ƙaruwa ya ke yi a ƙarƙashin mulkin sa. Babu tsaro a jihar sa ta haihuwa, Katsina. Babu tsaro a Zamfara da Sokoto da Kebbi da Neja. Babu tsaro a wasu sassan jihar Kaduna da Arewacin Najeriya.

A karon farko tun bayan samun ‘yanci, taɓarbarewar tsaro ta haifar wa Bakatsine da Badauri da Zamfare da Basakkwace da Banufe yin hijira. Wasu ma a Jamhuriyar Nijar su ka yi dandazo.

Allah kaɗai ya san yawan mutanen da aka kashe a Katsina, mahaifar Buhari a tsaron shekaru shida da rabi da Buhari ke kan mulki. Kuma Allah kaɗai ya san waɗanda aka kashe a sauran yankunan Arewa.

4. Dawo da kamfanin jiragen sama ta ƙasa: Har yanzu dai jiya iyau. Sai dai mu ji a jawabai da hotuna amma har yanzu ba a kai ga tabbatar wannan magana shekaru bakwai kenan.

5. Rage Tsadar Fetur: Zuwa yanzu dai wannan alƙawari na Buhari bai ma kai tasirin mafarki ba. Baya ga ƙarin farashin fetur da aka samu a lokacin sa, a yanzu haka gwamnatin sa za ta cire tallafi a shekarar 2022, ta yadda litar fetur ɗaya za ta iya kaiwa N345.

6. Alƙawarin Gyaran Zaɓe: Wannan na daga sahun alƙawurran Buhari na farko. Sai dai kuma fatali da Ƙudirin Gyaran Dokar Zaɓe da Buhari ya yi kwanan baya, ya sa duk wani mai tunanin Buhari zai cika alƙawarin gyaran zaɓe ya daina wannan wannan mafarkin.

7. Alƙawarin Sauya Fasalin Najeriya: Wannan na daga cikin alƙawurran da shi da APC su ka yi kamfen cewa za su yi. Amma bayan an hau mulki cikin 2015 har zuwa yau, gwamnatin Buhari ta daina tayar da batun, kuma ba ta so ta ji ana tunatar da ita wannan alƙawari.

8. Alƙawarin Gyaran Matatun Mai: Wannan alƙawari tabbas APC ta yi kamfen da shi sosai, kuma ta karya lagon PDP ta hanyar yi wa talakawan Najeriya alƙawarin gyara matatun fetur na Warri, Fatakwal, Kaduna da Legas.

Shekaru kusan bakwai bayan mulkin Buhari ya ƙara narka biliyoyin kuɗaɗen gyara matatun mai, a yanzu dai alƙawarin ya zama tatsuniya.

Lamarin ya lalace har ta kai a yanzu gwamnatin Najeriya ta dogara ne da matatar mai wadda Dangote ke ginawa a Legas, domin ta riƙa samun fetur cikin sauƙi.

9. Alƙawarin Karya Darajar Dala: Buhari ya yi alƙawarin ƙara wa Naira daraja, yadda ko da ta ruƙume kokawa da dala, to ba za a ji kunya ba.

Maimakon haka, yayin da Buhari ya hau a lokacin da dala ɗaya ta na daidai da naira 197 zuwa 220. Amma a yanzu dala ɗaya ta kai naira 570.

10. Wasu Alƙawurra Da Dama: Irin waɗannan sun haɗa da alƙawarin sayar da bargar jiragen Fadar Shugaban Ƙasa, alƙawurran inganta lafiya, alƙawurran kewaye makarantun Arewa maso Yamma a gina masu katanta da waya da kuma sa masu ‘CCTV camera’ da alƙawarin kare ɗalibai daga sacewa, bayan an sace ɗaliban Chibok.

Maimakon a samu tsaro a makarantu, sai ya zama a tarihin ƙasar nan, a zamanin mulkin Buhari ne aka fi sace ‘yan makaranta ƙanana da manya zuwa har na jami’a.

Tags: AbujaAPCLabaraiNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

Dan takara zai iya lashe zabe a kasar Gambiya ko bai sami mafi yawan kuri’u ba? – Binciken DUBAWA

Next Post

YA GUDU BAI TSIRA: Shari’ar Saminu Turaki ta koma sabuwa, bayan tsaikon shekara 14

Premium Times Hausa

Premium Times Hausa

Next Post
Hukumar EFCC ta tsare Saminu Turaki

YA GUDU BAI TSIRA: Shari'ar Saminu Turaki ta koma sabuwa, bayan tsaikon shekara 14

Discussion about this post

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Gwamnatin Tinubu ta sanar da dakatar da harajin (VAT) kan man dizal na tsawon watanni 6
  • Matsayar da aka cimma a taron Gwamnatin Tarayya, NUC da TUC – Minista Idris
  • ‘Gyaran Najeriya sai a hankali, miji na ba da rauhanai ya ke aiki ba’ – Remi Tinubu
  • Ba ni kaɗai ne na fidda sunan Ahmed Lawan ya yi takarar shugaban kasa da Tinubu ba, akwai wasu da ke bayan fage – Adamu
  • Yadda bashin da Chana ta hana Najeriya ya kawo cikas a noman shinkafa, da aikin titin jirgin ƙasan Ibadan zuwa Kano

Abinda masu karatu ke fadi

  • auto verkopen on ZAMFARA: Mahara sun gudu sun bar bindigar harbo jiragen sama a dajin Gumi da Bukkuyum -Inji ‘Yan Sanda
  • Laser-Haarentfernung mit hygienischen Bedingungen und aktuellen Gesundheitsstandards in der Türkei on An yi min murɗiya ne a zaɓen APC, ban yarda ba sai an sake zaɓe – Korafin Bashir Ahmad
  • Call Girls Sehore on Ƙungiya ta yi kira ga gwamnati ta ware kuɗaɗe domin samar da dabarun bada tazarar Iyali
  • buy aged stripe account on Hukumar NBC ta gayyaci mai gabatar da shirin ‘Berekete’, bayan macen da ta kona gashin kan yarinya barkatai, ta sha mari barkatai a hannun sa
  • research and survey on Gwamnan Edo ya bijire wa umarnin kotu, ya ce sai mai shaidar rigakafin korona zai yi sallar jam’i a masallaci

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2023 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.