A wata kasaitacciyar biki da ya gudana a babbar birnin tarayyar Najeriya Abuja ranar Laraba 3 ga Nuwamba, an mika wa kakakin jihar Kaduna Yusuf Zailani kambun kakakin majalisa
Kakakin Majalisar Kaduna Yusuf Zailani ya samu karramawar daga talbijin din Igere TV wanda ke shirya irin wannan karramawa duk shekara.
Zailani ne yayi zarra cikin duka kakakin majalisun kasar nan 36.
A cikin makon jiya, Igbere TV ta bayyana sakamon zaben ta yi wanda ya nuna Zailani ne aka zaba acikin duka kakakin majalisun Najeriya.
An bayyana Zailani a matsayin mutum mai kowa na shi. Baya ga kyauta da taimako da aka shede shi dashi yana da matukar farin jini a jama’a.
Da yawa daga cikin wadanda suka tofa albarkacin bakin su game da wannan karramawa da akyi wa Zailani a wannan shekara, sun ce abin ya zo a daidai ne.
Wani dan majalisa da baya so a ambata sunan sa, ya bayyana cewa a nashi ra’ayin ba a taba samun kakakin majalisa da ake so kuma ya kware a aikin sa a jihar Kaduna kamar Zailani tun daga 1999 ba.
” Banyi mamakin lashe wannan kyauta da yayi ba. Zailani ya saita majalisar jihar Kaduna, sannan kuma ya kara karfafa dankon zumunci tsakanin majalisar da bangaren zartaswa karkashin gwamna Nasir El-Rufai. Kuma gashi duk kasa ana shaidar sa da tausayi, rikon amana, kyauta da taimakon al’umma” In ji wani dan majalisan Kaduna.
A karshe ya ce wannan nasara ce h=ga majalisar jihar da kuma jihar Kaduna baki daya.