• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

    GUDUN YIN BIYU-BABU: Gwamnan Bauchi ya sayi fam ɗin sake yin takarar gwamna, daidai lokacin da ya fito takarar shugaban ƙasa a PDP

    Farin jinin Buhari da mara min baya da yayi ya sa na samu daukaka a siyasa – Bala Mohammed

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

Shin da gaske ne kaifin kwakwalwar mace kan yi rauni a lokacin da take dauke da juna biyu? Binciken DUBAWA

Silas JonathanbySilas Jonathan
November 2, 2021
in Kiwon Lafiya
0
KANJAMAU: Akalla mata masu ciki 124,817 ke dauke da cutar a Kanjamau jihar Ondo

Pregnant Woman

Zargi: Wani mai amfani da shafin Tiwita na zargi wai kwakwalwar mace kan yi rauni duk lokacin da ta ke da juna biyu kuma ya kan bukaci akalla watanni 6 kafin ya koma yadda ya ke kafin ta yi cikin.

Siffar jikin mace wakilci ne na yadda ta ke tunanin jikinta da halinta da ma yadda ita kanta take tunanin kamanninta wanda ya samo asali daga halitta, tunani da kuma tasirin yanayin zamantakewar dan adam. Duk wadannan abubuwa ne da sauyin da mace kan fuskanta lokacin da ta ke da ciki kan nuna.

Domin a lokacin da jikin mace ke sauyawa wadansu daga cikin sauye-sauyen a bayyane suke irinsu girman ciki, da kiba a yayinda wasun su kuma ba kowa ne zai iya gani ba, alal misali, irin su fadadar mahaifa, ciwon baya da laulayi.

Sauran sauye-sauyen da mace kan gani sun hada da:

– Yawan zuwa yin bawali
– hajijiya
– Kumburin ciki
– Sauyi a fatar jiki
– Girman ciki
– Sauyi a farjin ta

Da sauransu

Sai dai kwanan nan mun yi kicibis da zargin cewa wai kaifin kwakwalwar mace kan yi rauni a lokacin da ta ke da ciki, kuma wannan batu ya yi ta yawo a WhatsApp. A Shafin UberFacts (@UberFacts) da ke Tiwita ne wannan zargi ya fito ranar 21 ga watan Oktoba 2021

Ire-iren sauyin da ake samu lokacin da mace ke da juna biyu

Ciki ya kan fara ne sadda kwan na mace ya hadu da maniyin namiji, sa’annan ya gungura a hade ya manna kan shi a jikin bangon mahaifar na mace domin ya fara girma. Yawancin mata ba su iya sanin dai dai lokacin da hakan kan faru amma a wasu matan kuma su kan ga jini kadan mai kama da wanda ake gani yayin da mace ke haila.

Akwai alamu da dama da ake dangantawa da juna biyu. Wadannan alamun su kan bayyana ne cikin makonnin farko na daukan ciki. Ko da shi ke ba duka alamun ne ake gani a lokaci guda ba, kuma ba lallai ne a lokacin da aka gansu su kasance alamun ciki ba, idan dai aka dauke dukkan su a tare ana iya hasashen cewa ciki ne. To sai daibisa bayanan masana kimiya ba a riga an tantance duk wani tasirin da ake zaton ciki na da shi a kan kwakwalwa ba duk abin da aka sani yanzu hasashe ne.

A yaushe kwakwalwa dan adam ke rage girma?

Tsufa yana sauya girman kwakwalwa da tsarin yanayin yadda jijiyoyin jini suke da ma yanayin fahimtar abubuwa. Lallai kwakwalwa na sauyawa yayin da mutun ke kara shekaru kuma akwai sauye-sauye kama daga kwayoyin halitta zuwa yadda suke rikida. Tasirin tsufa a kan kwakwalwa da fahimta na da yawa kuma akwai dalilai da dama. Yayin da kwakwalwa yake raguwa, musamman a bangaren da ake kira frontal cortex, wurin da ke kula da fahimta, halayya da daukar matsaya da dabi’un mutun a yanayin zamantakewa, sa’annan su ma jijiyon jinin suka fara tsufa har aka fara samun hawan jini akwai yiwuwar samun bugun zuciya wanda zai iya janyo rauni a cikin kwakwalwar.

Bisa bayanan wani rahoto, ba sabon abu ba ne a ga sauyi a kwakwalwa yayin da mutun ke kara yawan shekaru. Ita ma fatar da ke rufe kwakwalwa wanda ake kira cerebral cortex a turance ta kan rage kauri, kuma ana iya ganin hakan a bangaren da ake kira frontal lobe, wurin da ke ajiye abubuwan da akan tuna, abubuwan sosa rai, dabarar shawo kan matsaloli, cudanya da jama’a da kuma ayyukan motsa jiki. Ana kuma iya ganin wannan raguwar kaurin a temporal lobe wanda ke bayan kunnuwa, wanda shi ne ke taimakawa dan adam wajen gane kalmomi, magana, karatu, rubuta da ma hada kalmomi ta yadda za su yi ma’ana.

Bangarorin kwakwalwar da ke raguwa suna da jijiyoyi wadanda ke kama da bututu. Bututun ne ke kai bayanai daga kwakwalwa zuwa bangarori daban-daban na jikin dan adam, sa’annan su sake daukar wasu bayanan da bangarorin jikin mutun su kai kwakwalwa. Yayin da dan adam ke kara shekaru, irin wannan ma’amala tsakanin jiki da kwakwalwa kan ragu abin da ka iya janyo matsaloli da dama.

Bisa la’akari da irin wadannan bayanai, za’a iya cewa kwakwalwar mace mai juna biyu na raguwa?

Tantancewa

Shugaban sashen kula da mata masu juna biyu da asibitin uwa da yara na jihar Ondo Dr Ayodele Adewole ya ce hakan ba gaskiya ba ne “Babu gaskiya ko kadan a wannan batu, ba abin ya yi nisa da gaskiya kamar haka, karyace kawai aka shirga. Kwakwalwar mai juna biyu ba ta raguwa, tsufa ce kawai ke rage kwakwalwa kuma ba abin da ya hada juna biyu da kwakwalwa.”

A waje guda kuma, babban darektan likitoci na asibitin koyarwa a jami’ar kimiyyar lafiya (UNIMED) Dr Adesina Akintan ya ce kimiyya ba ta riga ta sami hujjojin da suka nuna haka ba.

“Ban san wannan zargi na cewa kwakwalwar mace kan ragu yayin da take da juna biyu, sa’anna wai yana bukatar watanni 6 kafin ya koma yadda ya ke ba, babu hujjojin kimiya da su ka tabbatar da wannan dan haka ni ban yadda ba, babu wani tushen kimiyya da zan iya kamawa dangane da wannan batun,” ya ce.

Wani binciken da aka wallafa a wata kasidar kimiyyar kwakwalwa ya ce akwai sauye-sauyen da kan afku a kwakwalwar mace yayin da ta ke da juna biyu. Binciken ya ce kwakwalwan kan ragu amma kaifin shi kan karu, domin a cewar binciken wannan sauyin na shirya mace ne ta yadda za ta tinkari kalubalen da ke zuwa da zama uwa.

Sai dai wani binciken kuma ya sake bayyana cewa yanayin kwakwalwar mace kan sauya baki daya sadda ta dauki cikin farko, kuma wadannan sauye-suayen za su kai tsawon shekaru 2. Wata kila wannan na nufin kwakwalwar kan sauya a fanninin da zai taimaka mu su misali wajen lakantar ire-iren bukatun jarirai ko kuma gano irin barazanar da kananan yara ka iya fiskanta. Ya kuma kara da cewa raguwar sinadarin grey matter, wato wani ruwan da ake samu a kwakwalwa ba lallai ne ya kasance abu mara amfani ba, zai iya yiwuwa alama ce ta dattijantaka ko kuma kwarewa.

A Karshe

Duk da cewa akwai binciken da ke fitowa dangane da wannan zargi babu hujjojin da ke bayar da tabbacin cewa kwakwalwar mace na rage kaifi a lokacin da take dauke da juna biyu har ma yana bukatar watanni shidda kafin ya koma yadda yake a baya.

Tags: AbujaDubawaHausaKwakwalwaLabaraiNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

HATTARA: Kada a fada tarkon masu zambar wai ana buga cacar samun bizar zama a kasar Canada – Binciken DUBAWA

Next Post

Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

Next Post
Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe – Nazarin DUBAWA

Abubuwan da ya kamata a sani game da tsarin amfani da dabaru biyu wajen yin rajistar masu zabe - Nazarin DUBAWA

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • LAUJE CIKIN NAƊI: Cikin awa 24 APC ta canja ranakun gudanar da zabukan fidda gwanayen ta
  • Duk ‘Deliget’ ɗin da ke jira in bashi kuɗi, ya taka ‘Zero’ ba zai samu ko sisi daga wuri na ba – Shehu Sani
  • IYA KUƊIN KA, IYA SHAGALINKA: Na janye daga takarar gwamnan Kaduna – Baba-Ahmed
  • EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe
  • Ƴan sanda sun damke malamin da yayi wa ɗalibar sa ƴar shekara 13 fyaɗe

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.