• PREMIUM TIMES |
  • Tallata Hajar ka |
  • Adireshin mu |
  • PTCIJ |
  • Dubawa
Premium Times Hausa
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
  • Labarai
    • All
    • Duniya
    Dino Melaye

    Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

    Dalilin da ya sa ƴan bindiga ke ci gaba da kai wa mutane hari a jihar Neja – SSG

    Yadda ƴan bindiga suka kashe mutum 11 a Zamfara a karshen makon jiya

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    SHUGABAN ƘASA 2023: ‘Yan takarar APC na jihohin ƙabilar Igbo sun yi taron jiran-gawon-shanun goyon bayan duk wanda ya samu tikiti a cikin su

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TAKARAR SHUGABAN KASA: Muna tare da kai a koda yaushe – Sarkin Katsina Abdulmumini ga Osinbajo

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    TA KICIME A APCn KADUNA: Ɓangaren Sha’aban ba su amince da zaben wakilan jam’iyyar APC da aka yi ba

    Yadda sojoji suka cafke gogarman masu garkuwa da mutane da wasu 150 a dazukan Zamfara da Katsina

    Askarawan Najeriya sun kashe ƴan bindiga 42, sun kama 20 sannan sun ceto mutum 63 da aka yi garkuwa da su – DHQ

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Yadda Tinubu ya taimake ni na zama gwamnan Jigawa -Badaru

    Crisis in Jos

    BAUCHI: Matasa sun babbake gidaje da shaguna da dama a Warji bayan Rhoda Jatau ta yi kalaman ɓatanci ga Annabi SAW

  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    CHAMPIONS LEAGUE: Ko dai tsinuwar Yaya Toure ta yi tasiri kan Pep Guardiola?

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    PILLARS SUN KIRA RUWA: Daga yanzu a Abuja za su rika wasan gida kuma an zaftare musu maki 3

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan  Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    Yadda Kanawa suka yi ragaraga da motar ƴan Katsina United saboda Pillars ta buga kunnen doki a Kano

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    GHANA vs NAJERIYA: Ko Najeriya za ta kauce wa ɗauko buhun kunya na 26 a hannun ‘Black Stars’?

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    Barcelona ta yi wa Madrid dukan kabarin kishiya, ba sani ba sabo ta zura mata kwallaye 4 babu ko ɗaya

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    ‘CHAMPIONS LEAGUE’: Yadda Benzama ya ceto Madrid daga rijiya gaba dubu, ya kori PSG kuma ya dawo da martabar sa a duniyar ƙwallo

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    YAƘIN UKRANIYA YA CI ƘUNGIYAR CHELSEA: ‘Zan sayar da kulob ɗin na sadaukar da kuɗin ga tallafin waɗanda yaƙin Ukraniya ya kassara’ -Abramovich, mai ƙungiyar kuma ɗan asalin Rasha

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    RASHA: FIFA da UEFA sun dakatar da ƙungiyoyin Rasha buga wasannin ƙwallon Turai da duniya baki ɗaya

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

    KYAUTAR NAIRA MILIYAN 2: Allah ya saka wa Ahmed Musa, ina kira ga ‘yan wasa na yanzu su yi tattali don gaba – Obiekwue

  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna
    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    KURUNKUS: Malami ya fito takarar gwamnan Kebbi, ya ce jama’ar jihar ne suka tilasta masa ya fito

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    2023: Ɗan takarar shugaban kasa, Rotimi Amaechi ya ziyarci masarautar Dutse

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    LABARI CIKIN HOTUNA: Yadda ƴaƴan jam’iyyar APC da dubban mutanen Kaduna suka yi wa Sanata Uba Sani goma ta arziki

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    BIDIYO: Shin zaka iya zama da mai dauke da cutar Kanjamau? – Ra’ayoyin mutane

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    Dalilin da ya sa muka yi tattaki har Dubai domin taya Aisha Buhari murnar zagayowar ranar haihuwar ta – Matan Gwamnonin Najeriya

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    BIDIYO: Yadda ‘yan bindiga suka rika jibga ta kafin a biya naira 50,000 kudin fansa – Dattijo Saidu Dabo

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    ‘Yan mata marasa aure sun fi matan aure amfani da magungunan takaita Iyali – Ma’aikatar Lafiya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: Kwalaben ruwan maganin rigakafin Korona sama da Miliyan daya da aka lalata a Abuja saboda sun gama aiki kafin a dirka wa ‘yan Najeriya

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

    BIDIYO: RIKICIN BILLIRI: Yadda muka rasa ‘yan uwa da dukiyoyin mu a rikicin sarauta – Galadiman Tangale

No Result
View All Result
Premium Times Hausa
No Result
View All Result

SHARI’AR GWAMNONI 36 DA GWAMNATIN TARAYYA: Kotu ta hana kwasar dala miliyan 418 daga kuɗaɗen gwamnoni a biya dillalan gada-gada

Ashafa MurnaibyAshafa Murnai
November 6, 2021
in Manyan Labarai
0
DALLA-DALLA: Yadda Gwamnatin Tarayya, Jihohi Da Kananan Hukumomi Suka Ratattake Naira Tiriliyan 3.88 Cikin Wata 6

Buhari and Governors

A ranar Juma’a ce Babbar Kotun Tarayya a Abuja ta dakatar da Gwamnatin Tarayya kwasar dala miliyan 418 daga asusun jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774, da nufin ta biya wasu dillalan gada-gada masu iƙirarin cewa sun yi wa jihohi da ƙananan hukumomi ayyukan adadin kuɗaɗen a shekarun baya.

Dillalan gada-gadar sun ce sun yi wa jihohi da ƙananan hukumomi aikin tuntuɓa ne da wasu kwangiloli tsakanin 1995 da 2002, wajen ƙoƙarin aikin dawo masu da kuɗaɗen da aka riƙa ɗibar masu ana biyan bashin Paris Club da London Club.

Babban Mai Shari’a Iyan Ekwo ya umarci Gwamnatin Tarayya ta dakatar da fara kwasar kuɗaɗen da ta shirya fara kwasa daga watan Nuwamba, har sai bayan an kammala shari’ar da Gwamnonin Najeriya 36 suka shigar a gaban sa.

Gwamnonin 36 sun shigar da ƙarar ta hannun gogaggun lauyoyin su biyu, Jibrin Okutedo da Ahmed Raji, waɗanda dukkanin su manyan lauyoyi ne (SAN).

A ƙarar da su ka shigar, lauyoyin sun shaida wa kotun cewa Gwamnoni 36 na Najeriya ba su yarda cewa waɗancan dillalan gada-gadar sun yi ayyukan da su ka ce sun yi a jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774 a shekarun baya ba.

Lauyoyin sun ce masu iƙirarin sai an biya su haƙƙin kuɗaɗen har dala miliyan 418, ‘yan gidoga ne kawai, lamarin babu gaskiya a ciki.

“Kuma idan Gwamnatin Tarayya ta kwashi kuɗaɗe a asusun jihohi 36, to jihohin za su kasance a talauce, ta yadda biyan albashi ma ba zai yiwu ba.”

Daga cikin waɗanda gwamnoni 36 su ka kai ƙara, har da Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ta Tarayya, Ma’aikatar Harkokin Shari’a da Antoni Janar, kuma Ministan Shari’a da kuma Ofishin Bin-diddigin Kuɗaɗen Bashi (DMO) da kuma Kwamitin Rabon Kuɗaɗen Kasa na Gwmnatin Tarayya, wato FAAC.

PREMIUM TIMES Hausa a baya ta sha buga wannan gurungunɗumar rikici.

Labarin baya-bayan nan da ta buga, shi ne wanda ɗaya daga cikin waɗanda ke neman a biya su kuɗaɗen, ya ce: ‘Gidoga Gada-gada Ce, Ba Sata Ba’: Ko kukan jini Gwamnoni 36 za su yi, sai an biya mu la’adar Naira biliyan 172 daga asusun su -Ted Nwoko, uban gada-gada.

Wani uban gada-gada kuma tsohon ɗan majalisar tarayya, sannan kuma hamshaƙin biloniya, Ted Nwoko, ya rubuta wa Ministan Shari’a Abubakar Malami wasiƙa, mai ɗauke da yin tofin tir ga wasiƙar da Gwamnonin Najeriya 36 su ka aika wa Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed, inda su ka nemi kada ta biya ‘yan gada-gadar gidoga dala miliyan 418, waɗanda Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannun amincewa a biya su, ba tare da neman shawarar gwamnonin ba.

Nwoko wanda shi ma lauya ne, ya aika da wasiƙar ta hannun lauyan sa Joe Gadzama, inda ya bayyana wa Antoni Janar Malami cewa wasiƙar gwamnonin cike ta ke da jahilcin yadda aka yi har ‘yan gidogar su ka cancanci a biya su kuɗaɗen a matsayin la’adar ayyukan da su ka yi wa jihohin Najeriya da ƙananan hukumomi 774 a baya.

Ted Nwoko wanda ya ce kuɗaɗen idan an biya, shi ke da dala miliyan 142 a cikin dala 418 da za a biya, ya ƙara da cewa ko kukan jini gwamnonin Najeriya za su yi, sai an ɓamɓarar masa kuɗin sa daga asusun su an biya shi.

Ted dai ya aika wa Malami wasiƙar a ranar 6 Ga Satumba, 2021, tare da nuni da cewa babu wani umarni ko hukunci a kotu wanda ya dakatar a biyan sa haƙƙin sa.

Cikin watan Agusta ne dai Shugaba Muhammadu Buhari ya yi biris da shawarar gwamnonin Najeriya, ya rattaba hannun amincewa a biya ‘yan gada-gadar su shida dala miliyan 418, kwatankwacin fiye da Naira biliyan 170.

Hannun da Buhari ya rattaba ne ya sa Ministar Harkokin Kuɗaɗe ta umarci Ofishin Kula da Basussuka na Ƙasa (DMO) cewa ya bai wa ‘yan gada-gadar takardun alƙawarin biyan su basussukan cikin shekaru 10.

Bibiyar Musabbabin Kwatagwangwamar Gwamnoni 36 Da ‘Yan Gada-gada 6:

Gwamnoni 36 sun gargaɗi Ministar Kuɗaɗe kada ta biya ‘yan gidoga’ kuɗaɗen.

Gwamnonin Najeriya 36 sun rubuta wa Ministar Harkokin Kuɗaɗe Zainab Ahmed Wasiƙa, inda su ka gargaɗe ta cewa kada fa ta sake ta biya dala miliyan 418 ga ‘yan kwangilar da gwamnonin su ka ce ‘yan gidoga na gidi.

Wasiƙar dai sun rubuta ta ne ta hannun lauyan su Femi Falana, wanda ya rubuta mata hatsarin da ke tattare da biyan kuɗaɗen.

Falana ya nemi a madadin gwamnonin cewa Minista Zainab ta janye umarnin da ta ba Ofishin Kula da Basussuka (DMO) cewa ya fara shirin bayar da takardun alƙawarin biyan kuɗaɗen a cikin wasu ƙayyadaddun lokuta ga ‘yan kwangilar.

Gwamnonin sun ce ya kamata Minista Zainab ta fahimci cewa sun shigar da ƙara a Kotun Ƙoli, kuma Kotun Ƙoli ba ta ce a biya kuɗaɗen ba, domin harƙalla ce da dungu da gidoga kawai.

Kuɗaɗen waɗanda dala miliyan 418 ne, idan aka canja su zuwa dala a farashin gwamnati na dala 1 Naira 410, za su kama naira biliyan 171 kenan.

PREMIUM TIMES Hausa ta buga yadda Buhari ya yi fatali da shawarar Gwamnoni 36, ya amince a biya dala miliyan 418 da su ka ce gidoga ce ba bashi ba.

Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannun amincewa a biya wani bashin da aka yi iƙirarin ana bin jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774.

Adadin bashin ya kai dala miliyan 418, kwatankwacin naira biliyan 159 da ya amince a biya wasu mutum shida, duk kuwa da cewa Gwamnonin Najeriya sun daɗe su na nuna wa Buhari cewa babu tabbaci ko wata ƙwaƙƙwarar shaida ko hujjar an yi ayyukan a jihohi har na waɗannan adadin maƙudan kuɗaɗe.

A ranar Talata PREMIUM TIMES ta ci karo da wani umarni da Ma’aikatar Harkokin Kuɗaɗe ta bai wa Ofishin Kula da Basussuka (DMO), cewa ya fara bayar da takardar alƙawarin biyan kuɗaɗe ga waɗanda su ka yi iƙirarin cewa su na bin jihohin da ƙananan hukumomi waɗannan kuɗaɗen.

Hakan dai ya na nufin Shugaba Muhammadu Buhari ya rattaba amincewa a biya bashin kenan.

Wannan mataki da Buhari ya ɗauka ya saɓa da shawarar da Gwamnonin Najeriya su ka sha bayarwa cewa a fara gudanar da ƙwaƙƙwaran bincike a ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan, domin a tabbatar da sahihancin ayyukan da masu iƙirarin bin bashin su ka ce sun yi, amma ba a biya su ba.

Sai dai kuma duk da wannan damuwa da gwamnonin su ka nuna, Buhari ya amince a biya kuɗaɗen tare da yin fatali da shawarar ta su.

Za a biya su kuɗaɗen a tsawon shekaru 10, wato daga nan zuwa 2031. Za a riƙa cira daga cikin kuɗaɗen da Gwamnatin Tarayya ke bai wa Jihohi da Ƙananan Hukumomi duk bayan wata ɗaya.

Wasiƙar umarnin da aka ba Ofishin DMO dai an rubuta ta ne a ranar 12 Ga Agusta, 2021. Dama kuma tun a ranar 11 Ga Janairu Buhari ya amince a fara biyan kuɗaɗen, amma wata tankiya da gwamnoni ta sa ya dakatar.

Waɗanda za a biya kuɗaɗen dai su shida sun haɗa da tsohon Ɗan Majalisar Tarayya Ned Nwoko, wanda ya ke kafa hujja da umarnin biyan wanda Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta bayar a ƙarar da su ka shigar mai lamba FHC/ABJ/CS/148/2017.

Nwodo na neman a biya shi dala miliyan 142,028,941.

Sai kuma wasu mutum uku da ke neman a biya su dala miliyan 143,463,577.76 a ƙarar da su ka shigar mai lamba FHC/CV/2129/2014.

Su ukun sun haɗa da Riok Nigeria Ltd, Orji Nwafor Orizu da wani mai suna Olaitan Bello.

Wanda ya fi saura kason kuɗaɗe a cikin su shi ne Iseghoghi Edwards, mai dala miliyan 159. A bisa hukuncin da Babbar Kotun Tarayya ta Abuja ta zartas mai lamba FCT/CV/1545/2015.

Akwai kuma kamfanin wani mai suna George Uboh, wanda zai karɓi dala miliyan 47,831,920.

Salsalar Zargin Gidogar Da Gwamnonin Najeriya Su Ka Ce An Tafka A Batun Biyan Bashin:

Gwamnonin sun nuna damuwa kan yadda Minista Malami ya ƙi jin gargaɗin zargin harƙalla, ya riƙa ƙoƙarin a biya bashin naira biliyan 159.

An shafe shekaru ba ɗaya ba, ba biyu ba, Ministan Shari’a Abubakar Malami na bijire wa gargaɗin da ake yi masa cewa wasu kuɗaɗe da ya ke ta ƙoƙarin ganin an biya daga cikin kason kuɗaɗen Jihohi da Ƙananan Muhumomi har dala milyan 418 (naira biliyan 159), akwai gidoga a cikin lamarin.

Kuɗaɗen dai an ce wai bashi ne wasu ‘yan kwangila da jami’an tuntuɓa ke bin jihohi da ƙananan hukumomi.

Amma duk da gargaɗin da aka rika yi wa Malami, ciki kuwa har da rahoton da EFCC ta damƙa masa, wanda ta nuna cewa bashin haramtacce ne, ba gaskiya ba ne, shi kuma Minista Malami ya rufe ido sai matsa lamba ya ke yi domin ganin an biya waɗanda aka ce wai su na bin bashin, ta hanyar riƙa cirar kudade ana biyan bashin daga kuɗaɗen da Gwmnatin Tarayya ke bai wa Johohi da Ƙananan Hukumomi a duk ƙarshen wata.

Wannan jarida ta mallaki kwafe-kwafe na takardun da su ka riƙa karakaina da ke nuna yadda Malami ya rufe ido ya ke ta sharce gumin ganin lallai a biya kuɗaɗen, duk kuwa da cewa hatta Ƙungiyar Gwamnoni ta Najeriya, NGF ta bayyana masa cewa binciken ƙwaƙwaf ne kadai zai iya tabbatar da sahihancin bashin ko bogi da gidoganci ne kawai.

‘Yan Ƙaƙuduba Uku:

Sauran mutane biyun da su ka haɗa kai da Minista Malami domin ganin an biya kuɗaɗen ido-rufe, sun haɗa da Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari da kuma Ministar Harkokin Kuɗaɗe, Zainab Ahmed.

Gungun Wasu ’Yan Gidoga:

Wato akwai wasu ’yan dillancin gidoga da ke iƙirarin su ne wakilan masu bin bashin, waɗanda wakilan mu su ka ji cewa sun yi ƙoƙarin su bai wa Shugaban Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya, Kayode Fayemi toshiyar bakin dala milyan 40, domin ya haƙura, ya daina tirjiya, ya amince a biya bashin kawai.

Amma Gwamna Fayemi dtin na Jihar Ekiti bai amince ba, ya ƙi karɓar tayin da su ka yi masa, inda ya tsaya kai da fata cewa lallai sai dai a yi ƙwaƙƙwaran binciken ƙwaƙwaf domin a gano gaskyar lamarin.

Sai dai kuma bayan da PREMIUM TIMES ta fallasa wannan ƙaƙudubar, an riƙa ɗaukar nauyin buga wasu bayanan ɓata suna ga Gwamna Fayemi a cikin kafafen yaɗa labarai.

Cewa aka riƙa yi wai Fayemi an ƙi amincewa da roƙon da ya yi na a datse kashi 10 cikin 100 na bashin.

Salsalar Wannan Hukuncin Biyan Bashi:

Batun wannan bashi da ake tankiya da tababar sa, ya samo asali ne daga wani hukuncin da kotu ta yanke cewa wasu ’yan kwangila da jami’an tuntuɓa na bin jihohi da ƙananan hukumomi 774 na ƙasar nan basussuka.

Wasu ’yan gidoga su ka yi iƙirarin cewa su jami’an tuntuɓa ne su ka ce sun taimaka wa ƙananan hukumoni da jihohi domin su karɓo kuɗaɗen su da aka cira fiye da kima tsakanin 1995 da 2002 domin biyan bashin Paris Club.

Wasu ‘yan kwangila kuma daga cikin su wai sun yi wa ƙananan hukumomi 774 ayyuka bashi, saboda zaman jiran tsammanin za a biya kuɗaɗen Paris Club a biya su daga ciki.

A baya PREMIUM TIMES ta buga labarin yadda Shugaban Ƙungiyar Shugabannin Ƙananan Hukumomin Najeriya, ALGON ya nuna goyon bayan a biya kuɗaɗen.

Buhari Ya Sani Ya Yi Shiru:

PREMMIUM TIMES ta buga labari a cikin Janairu, yadda Ƙungiyar Gwamnonin Najeriya ta kai wa Shugaba Muhammadu Buhari ziyara tare da sanar da shi cewa cewa kada ya bari a biya kuɗaɗen, domin babu wata ƙwaƙƙwarar hujjar an yi ayyukan bashin.

Sai dai kuma duk da wannan gargaɗin Buhari bai taka wa su Malami burki ba

Sai ma da ta kai ga Malami ya samu saƙonnin gargaɗi daga wurare uku, ciki har da EFCC su na shaida masa cewa kada ya shiga gaba a biya bashin, domin akwai gidoga a cikin lamarin.

Cikin waɗanda su ka gargaɗi Minista Malami har da Shugaban ALGON na baya-baya, wanda shi ma ya nuna cewa kamfanonin tuntubar masu cewa su ne dillalan waɗanda ke bi bashi, ba su san da zaman su ba.

Yayin da su Malami su ka matsa lamba har Buhari ya sa hannu kan cakin kuɗin alƙawarin biya (promisory note), a ranar 4 Ga Disamba, 2020, su ma Gwamnomin daga baya cikin Janairu sun samo wani sabon umarni daga Buhari cewa kada a biya kuɗaɗen, har sai an yi ƙwaƙƙwaran bincike. Amma yanzu kuma Buhari ya amince a biya kuɗaɗen, ba tare da ya koma ta kan shawarar da Gwamnonin Najeriya su ka ba shi ba.

Ƙaryar Kwaram-kwaram Ta Ƙare:

Yanzu dai duk wani ƙoƙari da Gwamnonin Najeriya da Shugabannin ALGON 774 na Ƙananan Hukumomin Kasar nan kakaf su ka yi don kada a biya kuɗaɗen, ya tashi a iska, domin alƙalami ya bushe, tunda Shugaba Muhammadu Buhari ya sa hannun amincewa a biya kuɗaɗen.

Tags: AbujaGwamnoniHausaNajeriyaNewsPREMIUM TIMES
Previous Post

ZAƁEN GWAMNAN ANAMBRA: Muhimman Abubuwan Da Suka Faru Daga Ƙarfe 11 Zuwa 12:30 Na Ranar Zaɓe

Next Post

Sakamakon Zaɓen Anambra: APC, PDP da APGA sun fara kokuwar wawuran kuri’u

Next Post
Sakamakon Zaɓen Anambra: APC, PDP da APGA sun fara kokuwar wawuran kuri’u

Sakamakon Zaɓen Anambra: APC, PDP da APGA sun fara kokuwar wawuran kuri'u

Binciko

No Result
View All Result
Karanta

Ramadan Kareem AD

Sabbin Labarai

  • Dino Melaye ya sha ƙasa a zaben fidda gwani na jam’iyyar PDP a Kogi
  • LAUJE CIKIN NAƊI: Cikin awa 24 APC ta canja ranakun gudanar da zabukan fidda gwanayen ta
  • Duk ‘Deliget’ ɗin da ke jira in bashi kuɗi, ya taka ‘Zero’ ba zai samu ko sisi daga wuri na ba – Shehu Sani
  • IYA KUƊIN KA, IYA SHAGALINKA: Na janye daga takarar gwamnan Kaduna – Baba-Ahmed
  • EFCC ta cafke Okorocha bayan mamaye gidan sa da jami’an tsaro suka yi tun 11 na safe

Abinda masu karatu ke fadi

  • Google on Masarautar Kano: Hassada Ta Sa Wasu Na Neman Wofintar Da Kokarin Su Danfodiyo! Daga Imam Murtadha Gusau
  • Kuşburnu Çekirdek Yağı on Dalilin da ya sa muka yi sallar Idi ranar Laraba a Bauchi, muka ki bin sanarwar Sarkin musulmi – Sheikh Dahiru Bauchi
  • Google on HARKALLAR BILIYAN 3.6: Ba nine Balan da ke jerin sunayen masu mallakin kamfanin Adda ba – Gwamna Bala
  • Google on SIYASAR ZAMFARA : Maitaimakawa tsohon dan takarar gwamna a APC akan harkar jarida ya sauya sheka
  • Google on RAMIN MUGUNTA: Yadda Boko Haram suka afkawa bam din da suka dana wa Sojojin Najeriya

Fanni

Tweets by PTimesHausa
  • All Homepage Blocks
  • Home
  • Home
  • Main Home

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.

No Result
View All Result
  • Labarai
  • Labarai daga Jihohi
  • Wasanni
  • Kiwon Lafiya
  • Nishadi
  • Bidiyo da Hotuna

© 2022 JNews - Premium WordPress news & magazine theme by Jegtheme.