Gwamna Inuwa Yahaya na Jihar Gombe ya zargi tsohon gwamnan jihar, Ɗanjuma Goje da laifin haddasa mummunar tarzoma a jihar.
Gwamna Yahaya ya zargi Goje, wanda a yanzu sanata ne, a cikin wata ganawa da ya yi da manema labarai, jim kaɗan bayan ya gana da Shugaba Muhammadu Buhari, a Fadar Gwamnatin Tarayya, Abuja a ranar Talata.
Wannan furuci na Gwamna Yahaya ya zo ne kwanaki kaɗan bayan wata mummunar arangama da aka yi tsakanin magoya bayan gwamnan da na Sanata Goje.
Ƙazamin faɗan dai ya haddasa rasa rayukan mutum biyar.
Yayin da Goje ya zargi Gwamna Yahaya cewa shi ya shirya kai wa tawagar sa hari, inda magoya bayan gwamnan su ka hana Goje shiga Gombe, ita kuwa jam’iyyar APC reshen jihar Gombe, ta yi wa Goje barazanar cewa ya bai wa Gwamna haƙuri, ko kuma ta dakatar da shi daga jam’iyyar APC a jihar.
Da ya ke wa manema labarai jawabi, Inuwa Yahaya ya ce yanzu komai ya dawo daidai a jihar, tun bayan arangamar da aka yi.
Ya ce jama’ar Gombe sun bijire wa Goje ne, wanda a baya aminin sa ne na ƙut-da-ƙut da kuma na siyasa.
“Sanata Ɗanjuman dai da ku ka sani, shi ne ya haddasa rikicin, har ta kai ga an rasa rakuya kuma an lalata dukiyoyin jama’a.
“Mu dama abin da mu ke gudu kenan. Kowa ya san Goje ne ya kafa ‘yan kalare a Gombe, waɗanda suka riƙa kashe mutane.
“To ni ba zan amince da ‘yan kalare a Gombe ba. Kuma duk mai hannu a Kalare tilas ba za mu bari ya biya buƙatar sa da su ba. Da yardar Allah sai mun kawo ƙarshen kalare a Gombe.
An tambaye shi batun ƙorafin da Goje ya shigar Ofishin Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, inda ya ce wasu jami’an gwamnatin Gombe sun yi barazanar kashe shi, sai Gwamna Yahaya ya ce ai bincike zai tabbatar da gaskiyar zargin sa ko akasin haka.
An tambaye shi batun kokawar sake cin zaɓen sa a 2023, sai ya ce “Allah ne kaɗai ya san wanda zai kai shekarar 2023 ɗin, tsakanin sa da Goje.”
Discussion about this post