Kungiyar Ungozoma da ma’aikatan jinya ta Najeriya rashen jihar Katsina sun gudanar da zanga-zangar nuna bacin rai kan da yadda ‘yan sanda ke muzguna ma’aikatan jinya a jihar a lokacin aikin su.
Jami’an lafiyan sun fito sun gudanar da tattaki ranar Lahadi bayan ‘yan sanda sun ci zarafin wani ma’aikacin jinya dake aiki a babban asibitin Ahmadi Rimi dake Katsina.
Wani ma’aikacin jinya da yake ganawa da manema labarai Kamaludeen Kabir ya ce wannan ba shine karon farko ba da jami’an tsaro ke cin zarafin ma’aikatan jinya ba.
Kabir ya ce ‘yan sanda sun ci zarafin wani ma’aikacin jinya bayan sun kawo mutane biyu da suka yi hadari.
Yadda ‘yan sanda suka ci zarafin na
Ma’aikacin jinya Umar Lawal ya bayyana wa PREMIUMTIMES cewa a ranar Laraba da misalin karfe biyar na yamma ‘yan sanda suka shigo asibitin da nake aiki da wasu mutane biyu da suka yi hadari.
Lawal ya ce cikin gaggwa ya duba mutum na farko inda ya ga cewa mutumin ya ji rauni sosai, shi kuma mutum na biyu ma ya rasu tun kafin a kawo sa asibiti.
Ya ce daga nan sai ya bukaci ‘yan sandan su taimaka su siyo magani domin a kula da shi kada ya mutu.
” Daya daga cikin ‘yan sandan ya ce na duba aljihun mutumin na ciro kudin da za a siyo magungunan da ake bukata.
” Da na ciro kudin daga cikin aljihun mutumin sai na mika wa dan sanda domin ya siyo magani inda ya ce sai dai ni na je na siyo maganin ba su ba.
” Amma sai na ce masa hakan ba zai yiwu ba domin ina aiki.
” Fadin hakan da na yi sai dan sanda ya dauke ni da mari ni kuma na rama sannan sauran ‘yan sanda suka yi mun taron dangi suka yi min dukan tsiya.
“A cewar su dole na karbi kudi na je na siyo maganin da ake bukata ko kuma su kule ni a caji ofis. Da na ga da gaske suke sai na gudu zuwa cikin asibitin.
Discussion about this post