Majalisar Dattawa ta yi fatali da roƙon da Ma’aikatar Harkokin Lafiya ta Tarayya ta yi, inda ta nemi amincewa ta ciwo bashin dala miliyan 200 daga waje, domin sayo gidan sauron da za a raba a jihohi 13 da za a kori zazzaɓin maleriya.
Kwamitin Lafiya na Majalisar Dattawa ne ya ƙi amincewa da buƙatar, a lokacin da Babban Sakatare na Ma’aikatar Lafiya, Mahmuda Mamman ya yi masu bayanin cewa kuɗaɗen da za a sayo gidajen sauron ma ramto su za a yi.
Sanata Ibrahim Olomiegba, ɗan APC daga Jihar Kwara ya ce wannan Sagegeduwa ce kuwa dabarar rashin dabara.
Ya ce ai a cikin Kasafin 2022, an ware Naira miliyan 450 domin yaƙi da zazzaɓin cizon sauro. “Don me kuma za a nemi iznin mu a ce wai a ciwo bashin dala miliyan 200 a sayo gidajen sauro?
Tun da farko dai Mahmuda ya ce idan an sayo gidan sauron, za a raba su ne a jihohi 13 daga jihohi 36 na ƙasar nan.
Ya ce za a raba su ne a cikin ƙananan hukumomi 208.
A ƙarshe dai Sanata Abba Moro da sauran mambobin kwamitin su ka ce ba za a ciwo bashin ba. Waccan Naira miliyan 450 ta cikin kasafin 2022 ta wadatar.